• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Buhari Ya Dakile Barazanar Da APC Ke Fuskanta A Majalisar Dattawa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan majalisar dattawa na jam’iyyar APC guda 22 sun yi barazanar sauya sheka zuwa jam’iyyun PDP da LP da NNPP da dai sauran su, bisa kara fusatasu da aka yi sakamakon zaben fid da gwani da aka kammala.

Ganin haka ne ma ya sa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a ranar Talata ya roki sanatocin na APC kan kar su bar jam’iyyar domin kar ta rasa rinjaye a zauren majalisan dattawan Nijeriya.

  • 2023: Bayan Buhari, Dole Dan Kudu Ya Zama Shugaban Kasa – Fayose

Shugaba Buhari ya samu zama da wasu ‘yan majalisan dattawa na APC domin jin irin matsalolin da aka samu a wurin zaben fid da gwani da aka kammala. Ya dai amshi korafinsu tare da tabbatar da cewa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar za ta bi ba’asi a kan lamarin.

Ya bukaci ‘yan majalisan da su ci gaba da kokarinsu wajen ganin shugabancin jam’iyyar APC ya bunkasa kasar nan.

Ya ce, “Na ji dukkan korafe-korafenku kan zaben fid da gwani da aka kammala, zan yi kokarin ganin an share wa kowa hawayensa domin jam’iyyarmu ta ci gaba da iko a zauren majalisan dattawa da kuma babban zaben 2023. Ba za mu taba barin wannan barazanar ba tabbata ba.
“Akwai hanyoyin da za mu bi wajen warware duk wata matsa da ta kunno kai.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Wannan shi ne kyakkywan tsari a cikin dimokuradiyyarmu wanda muke gudanarwa. Tun daga lokacin da aka kammala zaben fid da gwani nake ta samun rahoto na korafe-korafe,” in ji shi.

A cewar mashawarcin shugaban kasa a fannin yada labarai, Femi Adesina, Shugaba Buhari ya sha alwashin karfafa shugabancin jam’iyyar APC ta hanyar yin adalci a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar kafin babban zaben 2023.

Shugaba Buhari ya fada wa sanatocin APC cewa samun nasarar jam’iyyar a babban zabe ya ta’allaka ne da yanayin hadin kan ‘ya’yan jam’iyyar da kaucewa rashin adalci a tsakaninsu.

Sai dai kuma Buhari ya gode wa ‘yan majalisan dattawan bisa bayar da shawaran gudanar da tattaunawa ta yadda za a su damar dinke bakin zaren na matsaloli da suka faru a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a lokacin zaben fid da gwani.

A nasa jawabin, shugaban tawagan kuma babban mai tsawatarwa na majalisar dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa a yanzu haka akwai a kalla sanatoci 22 da wasu mambobi na jam’iyyar ba su ji dadin abubuwan da suka faru a zaben fid da gwani da aka kammala ba a jihohinsu ba, saboda an gudanar da wasu lamari ba bisa ka’ida ba, wanda suka yi barazanar sauya sheka zuwa wasu jam’iyyun na daban.

Ya kara da cewa ‘yan majalisan dattawan sun sadaukar da kawunansu wajen ganin jam’iyyar ta bunka a cikin dimokuradiyyar kasar nan. Ya yi kira da shugaban kasa ya kawo daukin gaggawa kan wannan lamari.

Ya ce, “Mai girma shugaban kasa, tabbas a zauren majalisa mun yi aiki tukuru wajen ganin duk manufofinka sun gudana. Muna tabbatar maka da cewa a ko da yaushe muna goyon bayanka,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Tinubu Da Atiku Ba Za Su Iya Gyara Nijeriya Ba — Ango Abdullahi

Next Post

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bikin Cika Shekaru 25 Da Dawowar HK Kasar Sin Da Na Kaddamar Da Sabuwar Gwamnatin Yankin

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.