• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya sake caccaki takardun makarantar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

Atiku ya kalubalanci sahihancin takardar shaidar digirin Tinubu da jami’ar Chicago ta Amurka ta bayar, ya ce karatun shugaban kasar na ci gaba da zama babbar abun tantama.

  • Sakaci: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Asibitin Hasiya Bayero
  • Tottenham Da Chelsea Na Zawarcin Ansu Fati Na Barcelona

A wani sako da ya wallafa ta shafinsa na Tuwita, Atiku ya zargi shugaban kasar da kaurace kawo takardun karatunsa na firamare da sakandare amma sai ya kawo na digiri daga jami’ar Chicago.

A cewar tsohon mataimakin shugaban kasar, a shekarar 1999, Tinubu ya yi ikirarin cewa ya halarci makarantar firamare ta St. John’s da ke Aroloya a Legas, kafin ya wuce makarantar ‘Children’s Home’ da ke Ibadan.

Ya yi zargin cewa shaidar karatun Shugaba Tinubu a 2023 ya sha bamban da wanda aka gabatar a shekarar 1999, inda ya kara da cewa shugaban kasar ya ce ya halarci jami’ar Chicago ba tare da karatun firamare da sakandare ba.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

“Na farka da safiyar yau ina mamakin yadda muka sami wannan lamari. A cikin 1999, Tinubu ya yi ikirarin cewa ya halarci makarantar firamare ta St. John da ke Aroloya a Legas, kafin ya wuce zuwa makarantar ‘Children Home’ a Ibadan.”

“A cewarsa, ci gaba da karatu kwalejin gwamnati ta Ibadan da kwalejin Richard Daley da jami’ar Chicago ta Amurka.

“Abin mamakin shi ne, a 2023, Tinubu ya ce shi dai kwai ya halarci jami’ar Chicago kadai. Ina ta mamakin ko ta yaya hakan zai yiwu? Yana tunanin cewa ’yan Nijeriya ba za su shiga rudani ba kamar yadda na shiga cewa, Tinubu ba shi da takardar firamare da sakandare amma ya yi digiri a jami’a. Kuna iya tambayar Tinubu yadda ya samu wannan nasarar domin mu yi koyi da hazakarsa,” Atiku ya rubuta.

A watan Maris ne aka ayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2023. Amma Atiku ya ci gaba da kalubalantar sakamakon zaben a kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa, inda ya kalubalanci sahihancin takardun makarantar shugaban kasa.

Ya kuma garzaya wata kotun Amurka da ke gundumar Arewacin Jihar Illinois a Chicago, domin neman tilastawa jami’ar Chicago sakin bayanan karatun Tinubu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Japan

Goyon Bayan Da Amurka Ta Baiwa Japan Game Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba Shi Da Amfani

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.