• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Gudunmawar Addu’o’in ‘Yan Nijeriya Don Yaki Da Matsalar Tsaro — Badaru

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Muna Bukatar Gudunmawar Addu’o’in ‘Yan Nijeriya Don Yaki Da Matsalar Tsaro — Badaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan tsaro, Abubakar Badaru, ya roki ‘yan Nijeriya da su yi wa Allah su yi wa Annabi su ci gaba da taimaka wa gwamnati mai ci da tarin addu’o’i na musamman a bangaren tsaron kasa.

Badaru, wanda ya yi wannan rokon a Abuja yayin da ya karbi bakuncin wakilai daga jiharsa ta Jigawa karkashin jagorancin gwamna, Malam Umar Namadi, ya ce, duba da matsalar tsaro da ke addabar Nijeriya, akwai bukatar addu’o’i domin samun nasara a kan matsalar.

  • Badaru Na Da Kwarewar Jagorantar Ma’aikatar Tsaro – ANA
  • Kungiya Ta Jinjina Wa Tinubu Kan Nada Badaru Ministan Tsaro

A cewarsa, aikin da ke gabansu aiki ne jawur, don haka sun dukufa wajen shawo kan matsalolin kuma akwai bukatar gudunmawa da goyon bayan al’umar Nijeriya ta kowace fuska, ciki har da addu’o’i domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin kasar.

Da ya ke magana tun da farko, gwamnan jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, da ya jagoranci tawagar sarakuna, shugabannin addinai, ‘Yan kasuwa, ma’aikata da masu ruwa da tsaki daga jihar don kai ziyarar, ya ce, sun kawo ziyarar ne domin taya ministan murna tare da ba shi tabbacin goyon bayansu dari bisa dari a kowane lokaci.

“Ba fa iya zallar mu taya murna ne muka zo ba, a’a mun kuma zo ne domin mu yi maka addu’a. Mun san irin nasarorin da ka cimma a jiharmu, muna maka addu’ar za ka cimma irin wanan nasarar a wannan sabon matsayi da kake kai na ministan tsaro.” Cewar Namadi.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Gwamna Namadi ya tunatar da ministan irin tsammani da fatan da ‘Yan Nijeriya ke yi a kansa na cewa zai yi aiki tukuru domin shawo kan matsalolin tsaron da suke kasar nan, “Muddin ka cimma nasara a wannan bangaren, to kuwa ka taba kowani bangare a fadin kasar.”

“Mun yi nasara kuma mun ci sa’ar samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jiharmu ta Jigawa, hakan ba wai kuma yana nufin ba mu bukatar gudunmawarka ba ne, muna neman taimakonku da gudunmawarka domin ci gaban sauran jihohin kasarmu baki daya,” In ji Gwamnan Jigawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BadaruJigawaMinistan TsaroTsaroUmar NamadiZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilai Daga Kasashe Sama Da 90 Za Su Halarci Babban Dandalin Tattaunawa Na Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Karo Na 3

Next Post

Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

Related

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

36 minutes ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

2 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

2 hours ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

3 hours ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

6 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

7 hours ago
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.