• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Yanzu haka kasashe masu tasowa na samun ci gaba cikin sauri, inda suke samar da karin tasiri a duniya. Wannan wani yanayi ne mai yakini wanda ba za a iya sauya shi ba.” Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya fadi haka a kwanan baya, yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Zambia Hakainde Hichilema. Wannan zance ya nuna ra’ayinsa game da sauyawar yanayin da ake samu kan tsare-tsaren duniya.

Hakika ana iya ganin yadda kasashe masu tasowa suke samun karin karfi, bisa tantance wasu abubuwan da suka abku a kwanan baya. Misali, an shigar da kungiyar kasashen Afirka ta AU cikin rukunin kasashe masu karfin tattalin arziki ta G20, kana an yarda da sanya karin wasu mambobi 6 cikin tsarin hadin gwiwa na kasashen BRICS (Brazil, Rasha, India, Sin, da Afirka ta Kudu).

  • Birnin Shanghai Ya Karbi Bakuncin Bikin Yawon Bude Ido Na 34 Domin Bunkasa Fannin Yawon Shakatawa

Ban da haka, an gabatar da sabbin matakai na taimakawa kasashen Afirka cimma burinsu na dunkule tattalin arzikinsu waje guda, da zamanantar da kasashensu, wajen wani taron musayar ra’ayi na shugabannin kasashen Afirka da Sin.

Haka kuma, a wajen taron shugabannin rukunin kasashe 77 (wata kungiyar hadin gwiwar kasashe masu tasowa) da kasar Sin, da aka kammala shi jiya Lahadi a kasar Cuba, an gabatar da sanarwar karfafa hadin kan kasashe masu tasowa, da niyyarsu ta kara taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa. Duk wadannan abubuwa sun nuna karuwar karfin kasashe masu tasowa.

Sai dai babu shakka, wannan yanayi mai yakini da kasashe masu tasowa suke ciki zai janyo hassada, da kokarin hana ruwa gudu daga wasu kasashe masu sukuni. Hakan ya sa ake yin kokarin bayyana ra’ayin rashin amincewa da kashin dankali da ake yi a duniya, a wajen taron rukunin kasashe 77 da kasar Sin. Inda dimbin shugabanni, da manyan jami’ai na kasashe masu tasowa suka yi kira da a kawo karshen wani “ tsarin kasa da kasa mai cike da ayyukan kwatar dukiyoyi”, tare da bukatar dukkan kasashe masu tasowa da su gyara ka’idojin da ake bi yayin da ake tafiyar da harkokin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Ban da haka, sanarwar Havana da aka gabatar wajen taron ta nuna yadda ake kin yarda da tsare-tsaren duniya maras adalci, inda aka yi Allah wadai da matakan tilastawa sauran kasashe yin wani abu, da sanyawa kasashe masu tasowa takunkumi, da hana su samun damar raya fasahohi na zamani, da dai sauransu.

Dalilin da ya sa kasashe masu tasowa ke kin amincewa da tsoffin tsare-tsaren kasa da kasa, shi ne suna neman maye gurbinsu da wani sabon tsari mai adalci, wanda zai ba su damar kare moriyar kai, da neman samun ci gaban tattalin arziki ba tare da wata matsalar da aka haifar musu ba. Sai dai ta yaya za a iya cimma wannan buri? A wajen taron rukunin kasashe 77 da kasar Sin na wannan karo, bangaren kasar Sin ya ba da shawara cewa, da farko, a yi kokarin dogaro da kai, da magance yin fito-na-fito da sauran kasashe, da neman daidaita sabanin ra’ayi ta hanyar sulhu. Na biyu shi ne, a yi kokarin tabbatar da adalci yayin da ake kula da harkokin kasa da kasa, da kare moriyar kasashe masu tasowa, da sanya su zama masu fada a ji a duniya. Kana abu na uku shi ne, a yi karin hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, don tabbatar da ci gaban tattalin arzikinsu, da daga matsayinsu a duniya ta fuskar raya sabbin fasahohi da sana’o’i.

Hakika a wannan zamanin da muke ciki, karfin kasashen yamma a fannin tattalin arziki da siyasa na raguwa, don haka sun kara nuna halayyarsu ta son kai, da rashin hankali. Wannan ya sa kasashe masu tasowa ke bukatar yin hadin gwiwa a tsakaninsu, don magance a ci zarafinsu. Daga baya wannan yanayin da ake ciki ya sa muke ganin dimbin kasashe masu tasowa ke kokarin rufa wa juna baya a sassa daban daban, da fito da murya iri daya. Ta la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke kunsar mafi yawan kasashe da al’umma a duniyarmu, hadin gwiwar su zai tabbatar da hauhawar matsayinsu a duniya a kai a kai. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu Adawa Tsakanina Da Messi – Cewar Ronaldo

Next Post

Amurka Ba Ta Da Ikon Sukar Sin Game Da Yaduwar Miyagun Kwayoyi

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

2 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

3 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

4 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

5 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

6 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

1 day ago
Next Post
Mao

Amurka Ba Ta Da Ikon Sukar Sin Game Da Yaduwar Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.