• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Yi Katsalandan A Gwamnatin Ododo Ba – Yahaya Bello

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ba Zan Yi Katsalandan A Gwamnatin Ododo Ba – Yahaya Bello
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kogi mai barin gado, Yahaya Bello, ya yi alkawarin ba zai yi katsalandar a gwamnatin Usman Ododo ba.

“Babu wanda ya yi katsalandar a gwamnatina, domin haka b azan yi a na Ododo ba. Jama’a sun gamsu da ni. Ododo Ahmed Usman shi zai gudanar da gwamnati da kansa ko ta yi kyau ko mara kyau shi ne mai daukar alhakki,

  • Muna Rokon Shugaba Tinubu Ya Hana Ministoci Tafiye-tafiye Zuwa Kasashen Waje – Akpabio
  • An Haramta Shan Sigari A Wuraren Shakatawa Da Makarantu A Faransa

Bello ya shaida wa manema labarai na fadar gwamnati a lokacin da Ododo da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, suka amshi takardar shaidar samun nasarar zabe da suka gabatar wa Shugaban kasa, Bola Tinubu a fadarsa da ke Abuja.

Sai dai ya yi kira ga al’ummar jihar da su bai wa sabon gwamnati mai zuwa hadin kai.

Ododo da Uzodimma sun gabatar da takardar shaidar lashe zabe ga Tinubu domin nuna godiya da irin shugabancin da yake gudanarwa tun bayan da ya zama shugaban kasa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Ganduje, shi ne ya gabatar da takurdun shaidar ga Tinubu.

Da yake magana a kan nasarar da ya samu a wa’adi na biyu, gwamnan Jihar Imo, Mista Hope Uzodimma, ya ce nasarar da ya samu a zaben ranar 11 ga watan Nuwamba, ta kara tabbatar da nasarar da Shugaba Tinubu ya samu a zaben shugaban kasar da kuma yadda jam’iyyar APC ke kara samun karbuwa a wajen ‘yan Nijeriya.

Ya kara da cewa cewa, “Kun tuna cewa a zaben ranar 11 ga watan Nuwamba babbar jam’iyyarmu ta APC ta samu tagomashi kuma ta samu nasara a Jihar Kogi da kuma Jihar Imo, sannan jagoran jam’iyyarmu shi ne shugaban kasa. A bisa al’adar a duk lokacin da muka karbi takardar shaidar cin zabe a matsayin gwamnonin jihohin Kogi da Imo, dole ne mu karrama shugaban kasa ta hanyar kawo masa takardar shaidar basai irin shugabancinsa da jagorancin da ya nuna tun bayan hawansa shugabancin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji

Next Post

Yadda Majalisar Dinkin Duniya Ta Kammala Shirin Yaki Da Cin Zarafin Mata A Nijeriya

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

1 day ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Bello
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Yadda Majalisar Dinkin Duniya Ta Kammala Shirin Yaki Da Cin Zarafin Mata A Nijeriya

Yadda Majalisar Dinkin Duniya Ta Kammala Shirin Yaki Da Cin Zarafin Mata A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.