• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Bullar Sabuwar Annoba Ta Firgita Al’ummar Nafada A Jihar Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

A Karamar Hukumar Nafada da ke Jihar Gombe, wata sabuwar cuta ta barke wacce ta yi sanadiyyar rasuwar matasa sama da 30 ‘yan kasa da shekara 20 a duniya. Lamarin, wanda ya yi matukar ta da hankalin al’ummar yankin, musamman kan yadda har zuwa yanzu ba a gano hakikanin wace irin cuta ba ce, ya fi shafar yara ‘yan makarantar sakandare.

Wakilinmu ya zanta da masu ruwa da tsaki inda suka nuna matukar damuwarsu a kan wannan cuta. Koda-yake, tun da farko an yi zargin cewa, cutar Sankarau ce amma bayan gwaje-gwajen da jami’an kiwon lafiya suka yi, an gano cewa ba ita ba ce, kuma har zuwa yanzu dai ana ci gaba da bincike.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Ba Za A Iya Dakatar Da Dunkulewar Kasar Sin Ba

Malam Yusuf Isa Jigawa, da ya rasa dansa mai shekara 17 a duniya, Abdul’aziz Yusuf Isa; dalibi a Makarantar CGSS Nafada, ya shaida wa LEADERSHIP Hausa cewa, “Al’amarin nan, ya addabe mu a wannan yanki baki-daya. Mu dai a kashin kanmu, ba mu san wane irin ciwo ba ne kuma wannan ciwon idan ya samu yaro iyakar nisan zangonsa awa 24 ne, idan kuma ya wuce haka idan da rabo zai iya tashi. Amma mafi yawan su babu wanda ya wuce kwana guda”, in ji shi.

Da aka tambaye shi alamomin cutar, ya ce, “Ni dai nawa yaron ya fara kokawa kan cewa; kansa yana yi masa ciwo, daga maganar kansa na ciwo sai ya ce min kafarsa ma tana yi masa ciwo, daga kafa sai ya ce min cikinsa na ciwo, sai kuma kishirwa, yana bukatar ruwa a ba shi ruwa a ba shi ruwa, shi kenan sai aka ba shi ruwan, daga shan ruwa sai amai, bayan amai sai ya dan kwanta; jimawa kadan ya ce zai je bayan gida, amma ya kasa tashi. Duka-duka, wannan bai wuce awa guda ba ya kasa tashi, sai ni ne na dauke shi na kai shi.

“Bayan mun dawo, na tambaye shi cewa yanzu me yake ji? ya ce kafarsa yana ji kamar ana soka masa wutar lantarki. Bayan da muka ga abin ya wuce lissafi, sai muka dauke shi zuwa asibiti; nan ma ba abin da suka iya yi masa”, ya shaida.

Yusuf ya kara da cewa, jami’an kiwon lafiya sun yi gwaje-gwaje domin gano wace cuta ce, amma har yanzu ba a samu gano bakin zaren ba.

Malam Isa ya yi kira ga gwamnatoci da kungiyoyin kiwon lafiya da su kawo dauki zuwa wannan gari, domin dakile yaduwar wannan cuta.

Isa ya ce, a rana daya tak suna iya rasa yara sama da biyar, kuma kawo lokacin da aka zanta da shi babu wani rigakafin da jami’an kiwon lafiya suka yi musu, “Sannan, mafi yawan wadanda suka mutu matasa ne ‘yan kasa da shekara 22 zuwa kasa. Kazalika, an rasa yara sama da 50 a cikin kasa da wata biyu.” In ji shi.

Shi ma, Ali Bappa Alnafati, shugaban kungiyar bunkasa ci gaban Nafada, wanda shi ma ya rasa ‘yarsa mace, ya ce, babban abin da ke damunsu da ba a gano wace irin cuta ba ce da ke hallaka yara a wannan gari, wadanda mafi yawansu ‘yan sakandari ne.

“A yau da kuka same mu wurin amsar gaisuwar ta’aziyya, dan yayana mai suna Usmanu ne ya rasu. Ni ‘yata ita ce ta fara rasuwa wacce ta rasu a ranar 4 ga watan 2 na wannan shekara. Shi wannan ciwo ya yi nisa ne ya kai kwana biyu, idan ya kama yaro.

“Alamomin ciwon, sun hada da ciwon kai, ciwon kafa, idan yaro ya yi korafin ciwon kai to komai girmansa za a ga kafafunsa ba za su iya tafiya ba, sai an daga shi. Wadannan abubuwa su ne diyata ta yi fama da su, kuma ba ta kai awa 48 Allah ya karbi rayuwarta, haka sauran yaran ma. Haka shi ma wannan yaron Usman, ya ma yi hira da daddare lafiya kalau cikin dare ciwon ya kama shi, an fita za a kai shi asibiti da safe Allah ya karbi rayuwarsa.”

Kan adadin yaran da suka rasu ya ce, “Wallahi daga rasuwar ‘yata zuwa yau, mu je makabarta ba ku kirga ba za ku kirga yara 70 da suka rasu.”

A nasa bangaren, sakataren babban asibitin Karamar Hukumar Nafada, Kefas K. Sinna, ya bayyana cewa, “Gaskiya kam abu ya shigo mana kowa ma ya rasa meye ne ke tafiya. An fara kawo mana yaran nan da ciwon kafa da ciwon kai, ciwon kai din nan ma ba yadda za a kwatantashi da kuma ciwon ciki, wani lokacin kuma da amai.

“Mu a nan asibitin mutum bakwai ne muka yi recording din mutuwarsu, amma mafi yawa mutuwar kam a cikin gari ake yi. Daga farko mutum biyar ne daga baya kuma 2 suka karu a wannan asibitin. Tun daga nan kuma abun sai karuwa ya ke yi, ya yi sauki ya dawo ya yi sauki ya dawo.

“Likitoci sun yi aiki an dauki sample guda 20 an tura da tunanin cutar Sankarau ce, inda aka samu guda 11 ba cutar ba ce, yayin da muke cigaba da zaman jiran amsar guda tara,” sakataren asibitin ya tabbatar.

“Har yanzu ba a gano wacce irin cuta ba ce, sai dai muna bada shawarar kar a tsaya kan gwaje-gwajen cutar Sankarau zalla tun da ba a san menene musabbin ciwon ba. A dauki sample na jini, fitsari da na bayan gida a je a cigaba da bincike domin gano menene damuwar.’

Kefas ya tabbatar da cewa, likitoci na zuwa daga cikin Gombe su na kan aiki tukuru domin shawo kan cutar da neman mafita kan halin da ake ciki.

A zantawarsa da wakilinmu, Sarkin Nafada Dr. Muhammadu Dadum Hamza, ya yi kira ne ga al’ummar masarautarsa da a kowani lokaci su rika kai ‘ya’yansu zuwa asibiti domin tabbatar da an ba su agajin gaggawa a lokacin da suke cikin hali na rashin lafiya.

“An yi mace-mace kashi biyu. Na farko shi ne wadanda suka rasu a asibiti, akwai kuma wadanda suka rasa rayukansu a gida. A kuma bisa bayanan da muke samu wadanda suka rasu a gida sun fi wadanda suka rasu a asibiti yawa.”

“Maganar a zauna da marar lafiya a gida ba hanyace da take da kyau ba, asibiti shi ne gata kuma muna da asibiti. Don Allah don Annabi kada mutum ya zauna da marar lafiya a gida. Ba wai san rashin lafiyar ya tashi gagara sai a ce a je asibiti ba, tun da farkon abun ya kamata a je asibiti.”

Shi ma dan majalisar da ke wakiltar mazabar Nafada ta Arewa, Hon. Muhammad Tahir Dangaladiman Nafada, ya shaida ma wakilinmu cewa, tun lokacin da aka samu labarin cutar, ya je ya sanar da kwamishinan lafiya na jihar Gombe halin da ake ciki inda kwamishinan a cewarsa ya tura jami’ai domin a dauki gwaji domin gano wacce irin cuta ce ke damun mutane.

Zuwa lokacin hada wannan rahoto dai gwamnatin jihar ba ta tabbatar da hakikanin cutar da ta barke ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Next Post

LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma’ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

8 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

9 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

9 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

10 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

13 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

13 hours ago
Next Post
LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma’ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci

LEADERSHIP Ta Jinjina Wa Shehu Isma'ila Mai Diwani Kan Shafin Dausayin Musulunci

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.