• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Ginin Kamfanin Haɗa Magunguna Na AMA-MED A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Uba Sani da shugabar kungiyar kasuwanci ta Duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonjo Iweala, sun kaddamar da ginin katafaren kamfanin hada magunguna (AMA Medical Manufacturing Plant, Limited) ranar Alhamis, a Kudenda da ke, Kaduna.

Dakta Ngozi ta bayyana cewa, kamfanin an samar da shi ne don kasuwanci da zai habaka jihar Kaduna, Nijeriya da ma Nahiyar Afirka baki daya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutane 61 A Wani Sabon Hari A Kaduna
  • Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne

Tun da farko, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, a yayin da ya ziyarci kamfanin AMA-MED, ya bayyana cewa, zuba jari a jihar abin a yaba ne kwarai da gaske kuma hakan zai taimaka matuka wajen yaba kokarin gwamnatin jihar Kaduna na bunkasa harkar lafiya.

Gwamnan ya kara da cewa, kamfamin zai taimaka matuka wajen samar da damammaki masu yawa ga al’ummar jihar na daga samar da ayyukan yi, habaka harkar kiwon lafiya da dai sauransu.

AMA-MED

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

Uba Sani ya nuna cewa, jihar Kaduna ce ta daya kan saukin gudanar da kasuwanci a fadin Nijeriya.

“Muna da tsarin kasuwanci mafi inganci a jihar Kaduna, don haka mutane da dama suke zuwa don zuba hannun jarinsu a jihar, kuma ba ni da shakka a raina tare da haɗin gwiwarmu da AMA-MED, za mu sake jawo hankalin wasu masu zuba jari da yawa zuwa jihar.

“Muna da su daga Dubai, Indiya, Indonesia, Morocco wadanda suke tare da mu a jihar kuma a shirye muke mu yi aiki tare da AMA-MED, ba ni da wata shakka a raina, AMA-MED za su zama mafi kyawu kuma babban kamfani a fannin masana’antar kiwon lafiya a duk fadin Nijeriya.

Bikin ya samu halartar wakilan gwamnati, sarakunan gargajiya, manyan ‘yan kasuwa, fitattun masana daga cikin gida da kasashen waje da daidai sauransu.

Daga cikinsu akwai, Wakiliyar Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima; Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani; mataimakiyar gwamna, Dr Hadiza; Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate CON; Shugabar Kungiyar kasuwanci ta Duniya (WTO), Dakta Ngozi Okonjo Iweala; Sarkin Zazzau, Amb. Ahmed Nuhu Bamalli tare da wasu jami’an gwamnati.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AMA Medical Manufacturing LimitedJihar KadunaWTOZuba Jari
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Related

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

3 hours ago
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi
Labarai

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

4 hours ago
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
Labarai

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

4 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

5 hours ago
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
Labarai

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

6 hours ago
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
Labarai

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

7 hours ago
Next Post
Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

Matsanancin Rashin Lantarki Ya Addabi ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.