• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Da Ya Kamata A Sani Game Da Sabon Tsarin Biyan Kudin Wutar Lantarki

by Sadiq
2 years ago
Wutar Lantarki

Gwamnatin Tarayya ta sanar da karin kudin wutar lantarki da ‘yan Nijeriya ke biya, wanda hakan ya haifar da cece-kuce a tsakanin mutane.

Hukumar kula da wutar lantarki ta Nijeriya (NERC), ta yi karin kashi 240 cikin 100 na kudin wutar lantarki da ‘yan Nijeriya ke biya, inda ta ce hakan zai ba ta damar biyan kudin gas da kuma sauran gyare-gyaren injina da suka shafi rarraba wutar lantarki.

  • Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano
  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Digirin Bogi A Nijeriya – Minista

LEADERSHIP ta yi duba kan yadda sabon tsarin biyan kudin wutar lantarki zai kasance da kuma mutanen da ya shafa.

NERC ta kara farashin kudin wutar lantarkin kan Naira 225 kan kowane kilowat a awa daya, amma wannan kari zai shafi iya wadanda suke kan rukunin samun wuta na ‘A’ ne kadai.

Hukuncin dai na zuwa ne, daidai lokacin da ake fama da matsalar rashin wutar lantarki a fadin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Ga yadda tsarin biyan kudin wutar lantarkin zai kasance:

1.NERC ta amince da karin farashin wutar lantarki da kashi 240 ga kwastomomin da ke rukunin ‘A’, wanda kudin ya tashi daga Naira 66 zuwa Naira 225 a kowace awa daya.

2. Wannan karin ya shafi kwastomomin da ke samun wutar lantarki na awa 20 ko sama da haka, wadanda ke kan hanyoyin samar da wuta 481 daga 3,000, wanda ke wakiltar kashi 15 na mutanen da ke amfani da wutar lantarki a Nijeriya.

3. Masu amfani da wutar lantarkin da ba sa samun wutar awa 20 a rana, dole NERC za ta rage yawan abin da za su ke biya tare da sauya musu rukuni.

4. Wadanda suke kan rukunin ‘A’ za su fuskanci gagarumin karin farashin kudin wutar lantarki wanda zai iya tashi daga N50,000 zuwa N170,000 duk wata, amma ya danganta da yadda suka yi amfani da lantarkin.

5. Kwastomomin da ke kan rukunin ‘A’ ne kadai ke da tabbacin samun wutar lantarkin akalla awa 20 daga kamfanonin rarraba wutar lantarki guda 11, kamar yadda NERC ta bayyana.

6. Kwastomomin da ke kan rukunin ‘B’, ‘C’, ‘D’, da ‘E’, wadanda ke samun wutar lantarkin kasa da awa 20, karin kudin ba zai shafe su ba.

7. Karin kashi 240 na nufin gwamnati ta cire tallafin wutar lantarki gaba daya a kan kwastomomin da ke rukunin ‘A’, wadanda ke wakiltar kashi 15 na masu amfani da wutar lantarki, sannan kashi 40 na wutar lantarkin da ake rarrabawa a fadin kasar nan.

8. An kaddamar da karin ne a ranar Laraba, 3 ga watan Afrilu, 2024, wanda ke nufin kwastomomin rukunin ‘A’ ne kadai karin kashin 240 na wutar lantarki zai shafa.

9. Duk da karin kudin wutar lantarkin da aka yi, amma kwastomomi na fuskantar koma baya na samun wuta tun daga watan Janairu 2024, wanda ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ya danganta lamarin da karancin gas da ake fama da shi a kasar nan.

Sai dai wannan kari na kudin wutar lantarki da gwamnati ta yi, zai ta’allaka ne gaba daya da wutar da kwastomomi ke samu a rana, wanda da shi ne kadai za a yi alkalacin abin da za su biya duk wata.

10. Wadanda suke kan rukunin ‘A’ za a iya dawo da su wani rukunin matukar ba sa samun wutar lantarkin awa 20 a kowace rana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.