• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Da Ya Kamata A Sani Game Da Sabon Tsarin Biyan Kudin Wutar Lantarki

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Abubuwa 10 Da Ya Kamata A Sani Game Da Sabon Tsarin Biyan Kudin Wutar Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta sanar da karin kudin wutar lantarki da ‘yan Nijeriya ke biya, wanda hakan ya haifar da cece-kuce a tsakanin mutane.

Hukumar kula da wutar lantarki ta Nijeriya (NERC), ta yi karin kashi 240 cikin 100 na kudin wutar lantarki da ‘yan Nijeriya ke biya, inda ta ce hakan zai ba ta damar biyan kudin gas da kuma sauran gyare-gyaren injina da suka shafi rarraba wutar lantarki.

  • Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano
  • Za Mu Sa Kafar Wando Daya Da Masu Digirin Bogi A Nijeriya – Minista

LEADERSHIP ta yi duba kan yadda sabon tsarin biyan kudin wutar lantarki zai kasance da kuma mutanen da ya shafa.

NERC ta kara farashin kudin wutar lantarkin kan Naira 225 kan kowane kilowat a awa daya, amma wannan kari zai shafi iya wadanda suke kan rukunin samun wuta na ‘A’ ne kadai.

Hukuncin dai na zuwa ne, daidai lokacin da ake fama da matsalar rashin wutar lantarki a fadin kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Ga yadda tsarin biyan kudin wutar lantarkin zai kasance:

1.NERC ta amince da karin farashin wutar lantarki da kashi 240 ga kwastomomin da ke rukunin ‘A’, wanda kudin ya tashi daga Naira 66 zuwa Naira 225 a kowace awa daya.

2. Wannan karin ya shafi kwastomomin da ke samun wutar lantarki na awa 20 ko sama da haka, wadanda ke kan hanyoyin samar da wuta 481 daga 3,000, wanda ke wakiltar kashi 15 na mutanen da ke amfani da wutar lantarki a Nijeriya.

3. Masu amfani da wutar lantarkin da ba sa samun wutar awa 20 a rana, dole NERC za ta rage yawan abin da za su ke biya tare da sauya musu rukuni.

4. Wadanda suke kan rukunin ‘A’ za su fuskanci gagarumin karin farashin kudin wutar lantarki wanda zai iya tashi daga N50,000 zuwa N170,000 duk wata, amma ya danganta da yadda suka yi amfani da lantarkin.

5. Kwastomomin da ke kan rukunin ‘A’ ne kadai ke da tabbacin samun wutar lantarkin akalla awa 20 daga kamfanonin rarraba wutar lantarki guda 11, kamar yadda NERC ta bayyana.

6. Kwastomomin da ke kan rukunin ‘B’, ‘C’, ‘D’, da ‘E’, wadanda ke samun wutar lantarkin kasa da awa 20, karin kudin ba zai shafe su ba.

7. Karin kashi 240 na nufin gwamnati ta cire tallafin wutar lantarki gaba daya a kan kwastomomin da ke rukunin ‘A’, wadanda ke wakiltar kashi 15 na masu amfani da wutar lantarki, sannan kashi 40 na wutar lantarkin da ake rarrabawa a fadin kasar nan.

8. An kaddamar da karin ne a ranar Laraba, 3 ga watan Afrilu, 2024, wanda ke nufin kwastomomin rukunin ‘A’ ne kadai karin kashin 240 na wutar lantarki zai shafa.

9. Duk da karin kudin wutar lantarkin da aka yi, amma kwastomomi na fuskantar koma baya na samun wuta tun daga watan Janairu 2024, wanda ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ya danganta lamarin da karancin gas da ake fama da shi a kasar nan.

Sai dai wannan kari na kudin wutar lantarki da gwamnati ta yi, zai ta’allaka ne gaba daya da wutar da kwastomomi ke samu a rana, wanda da shi ne kadai za a yi alkalacin abin da za su biya duk wata.

10. Wadanda suke kan rukunin ‘A’ za a iya dawo da su wani rukunin matukar ba sa samun wutar lantarkin awa 20 a kowace rana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Karin KudiWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kashe Gobara Ta Ceto Mutane 12 Da Dukiyar Miliyan 130 A Kano

Next Post

Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

Related

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

3 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

5 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

5 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

20 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

1 day ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

1 day ago
Next Post
Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

Bloomberg: Damuwa Game Da Karfin Sin Wajen Samar Da Hajoji Ba Ta Da Tushe

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.