• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Manyan Attajiran Nijeriya A 2024

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
nijeriya

Kafar yada labarai ta Forbes ta bayyana sunayen wadanda suka zama attajirai mafiya arziki a Nijeriya a shekarar 2024. Su ne: Aliko Dangote, Mike Adenuga, Abdulsamad Rabiu, da Femi Otedola.

Kafar ta bayyana cewa Arzikin Dangote ya haura zuwa Dala biliyan 13.4, na Adenuga ya kai Dala biliyan 6.7, yayin da Abdulsalam Rabiu yake da Dala biliyan 5.2 shi kuma Otedola yake da dala biliyan 1.4.

  • Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba
  • Bata Gari Sun Daka Wa Motar BUA Wawa A Kan Hanyar Zariya

Aliko Dangote shi ne mutumin da ya fi kowa kudi a Nahiyar Afirka kuma bakar fata mafi arziki a duniya, inda aka kiyasta kudinsa ya kai kusan dala biliyan 13.4 a shekarar 2024. Katafaren kasuwancinsa na rukunnan kamfanin Dangote Group, na daya daga cikin manyan kamfanoni masu zaman kansu a Nijeriya kuma kamfani mafi daraja a Afirka ta Yamma.

Shi kuwa Mike Adenuga hamshakin attajiri dan Nijeriya ya yi shuhura ne da Kamfaninsa na Globacom, kamfanin sadarwa na biyu mafi girma a Nijeriya wanda har ila yau yake da ressa a Ghana da Benin. Haka nan Mike yana da hannun jari a Bankin Ekuitorial Trust da kamfanin hakar mai na Conoil (wanda a da ake kira Consolidated Oil Company). Forbes ta kiyasta darajar arzikinsa ta kai dala biliyan 6.7 a 2024.

A bangaren Abdulsamad Rabiu, hamshakin attajirin kuma mai bayar da agaji kuwa, shi ne wanda ya kafa kuma yake shugabantar rukunin kamfanonin BUA Group, wadda ke maida hankali kan masana’antu, ababen more rayuwa, da noma da kuma samun kudaden shiga sama da dala biliyan 2.5.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Femi Otedola hamshakin dan kasuwa ne a Nijeriya wanda yake shugaban kamfanin Lantarki na Geregu Power Plc. Har ila yau, Otedola ne ya kafa Kamfanin mai na Zenon Petroleum and Gas Limited, kuma shi ne ya mallaki wasu kamfanoni da dama da suke hada-hadar jigilar kayayyaki, gidaje, da kudi. A baya-bayan nan ya zuba jari a fannin samar da wutar lantarki a wani bangare na ‘yantar da fannin a Nijeriya.

A cewar Forbes, shekara guda kenan da attajiran duniya, wadanda arzikinsu ke ci gaba da tabarbarewa yayin da kasuwannin hada-hadar hannayen jari na duniya ke cikin ka-ka-ni-ka-yi saboda rikicin siyasa, da hauhawar farashin kayayyaki.

“Kamar yadda yake a tsarin tattalin arziki gaba daya, an fi mayar da hankali ne wurin tattara bayanan kudi. Yanzu an sami jerin mutane 14 da ke cikin da’irar hamshakai da suka mallaki dala biliyan 100, da kuma wasu hamshakai da arzikinsu ya kai kirgen lambobi 12. Hakan ya kasance ne a kimanin shekara hudu da suka wuce. Wadannan suna daga cikin kalilan da suka taki sa’a, inda darajar arzikinsu ta kai dala tiriliyan 2 gaba daya, ma’ana kashi 0.5 cikin dari kacal na attajirai 2,781 na duniya da suka mallaki kashi 14 cikin dari na dukiyoyin attajiran da ke doron kasa”. In ji kafar a rahoton da ta fitar.

Kafar ta kuma bayyana cewa, a halin yanzu an samu karin attajirai fiye da lokutan baya, inda ake da 2,781, an samu karin 141 idan aka kwatanta da yawansu a bara. Arzikinsu ya kai akalla dala tiriliyan 14.2 wanda aka samu karin dala tiriliyan 2 a kan na 2023.

Rahoton kafar ya kuma ayyana cewa Bernard Arnault shi ne ya ci gaba da rike kambunsa na hamshakin attajirin da ya fi kowa kudi a duniya. Attajirin mai kasuwancin kayan alatu dan kasar Faransa, an kiyasta yana da dala biliyan 233, inda ya samu karin dala biliyan 22 a kan abin da ya mallaka a 2023.

Amurka dai ita ce take da tarin hamshakan attajirai 813 wadanda arzikinsu ya kai dala tiriliyan 5.7, sai kasar Sin da take bi mata da yawan attajirai 473 da suka mallaki dala tiriliyan 1.7.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
kebbi

Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.