• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar NOUN Za Ta Bai Wa Hafsatu Abdulwaheed Da Innocent Chukwuma Digirin Girmamawa

NOUN Za ta yaye ɗalibai 22,175

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Jami’ar NOUN Za Ta Bai Wa Hafsatu Abdulwaheed Da Innocent Chukwuma Digirin Girmamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar NOUN za ta bayar da digirin girmamawa na dakta ga wasu hamshaƙan ‘yan Nijeriya biyu, wato Hajiya Hafsatu M.A. Abdulwaheed da Cif Innocent Chukwuma, a ranar Asabar 13 Ga Afrilun 2024.

Mataimakin Shugaban jami’ar, Farfesa Olufemi A. Peters, shi ne ya bayyana haka a wajen taron manema labarai da ya yi a Abuja a ranar Litinin kan bikin yaye ɗalibai karo na 13 da jami’ar za ta gudanar a ranar Asabar mai zuwa.

  • Kwamishinar Kidaya Ta Sadaukar Da Albashinta Na Shekara Don Karfafa Mata A Kaduna
  • Maganar Da Aka Taba Fada Min ‘Duk Marubuta ‘Yan Wuta Ne’ Ta Tsaya Min A Rai – Rukayya

Daraktan Yaɗa Labarai na jami’ar, Malam Ibrahim Sheme, ya faɗa a cikin takarda ga manema labarai cewa, ita dai Hajiya Hafsatu Abdulwaheed, ita ce mace ta farko a Arewacin Nijeriya da ta wallafa littafin hikaya, sannan sananniyar ‘yar gwagwarmaya ce mai rajin tallafa wa al’umma.

Littafinta, So Aljannar Duniya, an wallafa shi ne a cikin shekarar 1974.

Shi kuma Cif Chukwuma, shahararren ɗan kasuwa ne wanda ya assasa Innoson Motors, wanda shi ne kamfanin harhaɗa motoci na farko na ‘yan ƙasa da aka kafa a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

A taron manema labaran, Farfesa Peters ya ce, za a ba Hajiya Hafsatu Abdulwaheed digirin girmamawa na Daktar Wallafa ne (wato Doctor of Letters, honoris causa).

 

Ya ce: “Ta sadaukar da rayuwar ta ga hidimar haɓaka harkar ilimi, musamman na ‘ya’ya mata, bisa amanna da cewa, iya karatu da rubutu yana da ƙarfin sauya matsayin al’umma tare da karya lagon fatara da yunwa.”

Shi kuma Shugaban kamfanin Innoson Motors za a ba shi digirin ne a fannin Gudanarwar Kasuwanci (Business Administration) saboda ya ciri tuta a fagen “ƙirƙira, assasawa, tare da sadaukarwa ga amfani da kayan aiki na cikin gida.”

Ya ƙara da cewa ayyukan waɗannan mutane biyu da za a karrama “sun yi daidai da ainihin burukan NOUN na asali na haɓaka ilimin kasuwanci, samar da ababen ilimi, da kuma ƙirƙira.”

Jagoran jami’ar ya yi nuni da cewa NOUN ba ta cika bayar da digirin girmamawa ba, domin na ƙarshe da ta bayar tun cikin 1995 ne, saboda haka sai da ta yi zurfin tunani kafin ta yanke irin wannan shawarar.

Peters ya ce wannan girmamawar da za ta yi babbar nasara ce ga al’ummar jami’ar kuma hanya ce da za a samar da kyakkyawan haɗin gwiwa da ya ginu kan harkar ilimi.

Haka kuma jagoran ya bayyana cewa a bikin na bana jami’ar za ta yaye ɗalibai 22,175 waɗanda daga cikin su guda 15,768 masu digirin farko ne daga tsangayu takwas na jami’ar, sai 6,407 masu digiri na biyu, da ɗalibai shida masu digiri na uku.

Kafin ranar Asabar da za a yi bikin, za a ƙaddamar da sabon Shugaban Jami’a, wato Oba na Benin, Oba Ewuare II, a ranar Alhamis, kuma za a yi taron laccar yaye ɗalibai wadda Mataimakin Shugaban Buɗaɗɗiyar Jami’ar ƙasar Tanzaniya, Farfesa Elifas Bisanda, zai gabatar a ranar Juma’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Allah ya yi wa Jaruma Saratu Giɗaɗo (Daso) Rasuwa

Next Post

Za A Gurfanar Da Ganduje A Kotu Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa A Kano

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

8 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

9 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

9 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

10 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

12 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

13 hours ago
Next Post
Za A Gurfanar Da Ganduje A Kotu Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa A Kano

Za A Gurfanar Da Ganduje A Kotu Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.