• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kasar Sin Da “Wuce Misali” Ba Shi Da Tushe Ko Makama

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Kasar Sin Da “Wuce Misali” Ba Shi Da Tushe Ko Makama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cikin manyan batutuwa da sakatariyar baitil-malin Amurka Janet Yellen ta tabo, yayin ziyarar kwana kwanan nan da ta yi a kasar Sin, akwai zargin Sin da “Wuce Misali” a fannin bunkasa masana’antu masu alaka da makamashi mai tsafta, ciki har da na samar da ababen hawa masu aiki da lantarki.

Kafin ziyarar Yellen, kafafen watsa labaran Amurka sun yi ta yayata batun nan na “Wuce Misali” a fannin kere keren kasar Sin, suna zargin Sin din da cika kasuwannin duniya da kayayyakin fitarwa ketare masu rahusa, irin su farantan samar da lantarki ta hasken rana da ababen hawa masu aiki da lantarki.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Shugaban Kasar Mozambique
  • Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Neman Ra’ayi Kan Aikin Tattalin Arziki

To sai dai kuma, wadannan zarge-zarge ba su da tushe ko makama. Suna kuma fayyacewa duniya halayyar masu tsara manufofi na Amurka, dake da tunanin ko kasar su ta samu, ko kuma kowa ya rasa.

Karkashin irin wannan tunani ne mahukuntan Amurka suka kakaba takunkumin hana fitar da sassan laturori na kamfanonin kasar zuwa kasuwannin Sin, da hana wasu kamfanonin Sin din damar kasuwanci na halak ta fakewa da tsaron kasa.

Har ila yau, irin wadannan matakai na nuni ga matsayin Amurka na aiwatar da manufofi idan kawai za su yi daidai da moriyar kasar, da saba musu idan za su amfani sauran sassa. Wato dai a duk lokacin da masana’antun Amurka za su ci wata gajiya, kasar na yin “Uwa da makarbiya” wajen ganin sun cimma nasara, amma idan kamfanonin kasar za su yi takara da na sauran sassan duniya, sai Amurkan ta sanya shinge na baiwa kamfanoninta kariya, wanda hakan sam ya sabawa adalci.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

A gani na, maimakon zargin “Wuce Misali” kan kamfanoni masu alaka da makamashi mai tsafta na Sin, kamata ya yi ma Amurka da sauran kasashen duniya su goyi bayan ci gaban wannan fasahohi, duba da cewa a yanzu haka ana kan wata gaba da kasashen duniya ke ta kokarin sauya alkibla zuwa amfani da nau’o’in makamashi marasa gurbatawa da dumama yanayi.

A daya bangaren kuma, mun san cewa Sin da Amurka kasashe ne dake da bangarori da dama na hadin gwiwa da cin moriyar juna. Don haka ne ma har kullum, mahukuntan kasar Sin ke ganin abun da ya fi dacewa shi ne sassan biyu su ingiza ci gaban juna maimakon takawa juna birki, a dukkanin bangarori na ci gaba da aka saba da su na cinikayya, da noma, da ma sabbin fannoni irin su na kare yanayi, da fasahohi, da ayyukan kirkirarriyar basira ko AI.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Mallakar Zuciyar Maigida A Saukake

Next Post

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

22 hours ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

23 hours ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

1 day ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

1 day ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

1 day ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

2 days ago
Next Post
Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

LABARAI MASU NASABA

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

August 10, 2025
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.