ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na’urorin Kula Da Iyakokin Kasa Za Su Fara Aiki Ba Da Jimawa Ba – Ministan Cikin Gida

by Khalid Idris Doya
1 year ago
iyakokin kasa

Gwamnatin tarayya ta ce dukkanin iyakokin kasar nan an jibge musu na’urorin sanya ido masu sarrafa kansu domin inganta tsaron kasar da za su fara aiki nan ba da jimawa ba.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, shi ne ya shaida hakan a cikin makon nan a lokacin duba aikin da ake yi na ginawa da zuba kayan aiki a cibiyar kula da ba da umarni na mashiga ta fasahar zamani a filayen jiragen sama da kuma cibiyoyin tattara bayanai na kan iyakoki wadanda suke cikin shalkwatar hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS).

  • Ministan Kudin Zimbabwe Ya Jinjinawa Gudummawar Masu Zuba Jari Daga Sin
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Kira Taron Manema Labarai Game Da Halartar Shugaba Xi Jinping Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Tattauna Hadin-Kan Sin Da Kasashen Larabawa

Ya nuna gamsuwarsa da yadda ake gudanar da aiki mai inganci kuma cikin hanzari, ya lura kan cewa aikin farko na sanya na’uorin sa ido a iyakoki za su kammalu a watan Oktoban 2024.

ADVERTISEMENT

Ya sanar da cewa ginawa da sanya kayan aiki a cibiyar ba da umarnin da kula da ke NIS ya kammalu kaso dari bisa dari, wanda ana jiran kaddamar daga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu zai jagoranta. Ya kuma ce aikin sa ido kan iyakoki na zamani ya kai kaso 60 cikin dari na kammaluwa.

“Muna zaman jiran shugaban kasa ne domin kaddamarwa. TunI muka sanar da shugaban kasa kuma ina farin cikin sanar da ‘yan jarida cewa aikin an kammala shi 100 bisa 100.”

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

Tunji-Ojo ya kara da cewa tsarin sa ido kan iyakoki mai amfani da kansa na zamani zai taimaka wajen dakile aikata laifuka a iyakoki da kuma samun damar bibiyar iyakoki tun daga shalkwatar NIS kai tsaye.

Ministan ya jaddada cewa kula da tsaron iyakoki na da muhimmanci kuma na daga cikin muhimman abubuwan da Shugaban Tinubu ba zai yi sako-sako da su ba domin tabbatar da tsaro da kare ‘yan kasa.

Kwanturola janar na hukumar shige da fice, Kemi Nanna Nandap, ta bayyana cewa an horas da jami’ansu yadda za su tafiyar da sabbin na’urorin da ke aiki da kansa, inda ta ce a yanzu haka ma wasu jami’an na samun horo kan hakan.

Nandap ta kara da cewa al’ummomin da suke iyakokin kasar su ma an wayar musu da kai kan irin gudunmawar da ake fatan za su bayar domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba ciki har da bayar da muhimman bayanan da suka dace ga NIS a duk lokacin da bukatar hakan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
Labarai

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Labarai

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Next Post
nahcon

NAHCON Ta Karyata Rahoton Bayar Da Abinci Mara Inganci Ga Alhazai A Makkah

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.