• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ke Dagula Rashin Tsaron Nijeriya – Babban Hafsan Sojin Sama

by Leadership Hausa
12 months ago
in Manyan Labarai
0
Abin Da Ke Dagula Rashin Tsaron Nijeriya – Babban Hafsan Sojin Sama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban hafsan hafsa sojin sama, Air Marshal Hasan Abubakar ya danganta fafatawar da ake yi a tsakanin kasashen Amurka, Rasha da China a nahiyar Afirka, da kuma janyewar sojojin Jamhuriyar Nijar daga cikin rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa, a matsayin lamarin da ya kara ta’azzara kalubalen tsaro a yankin Sahel wanda ya haifar da kwararar makamai da ‘yan ta’adda zuwa Nijeriya.

Air Marshal Abubakar ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata ganawa da hafsoshin reshe da kwamandojin rundunar sojin sama da daraktoci da kuma daukacin manyan jami’an rundunar sojin saman Nijeriya a Abuja.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Sin Na Goyon Bayan Kokarin Kasashen Afrika Na Magance Matsaloli Ta Hanyar Da Suka Zaba

Da yake jawabi a wajen taron wanda ya zo daidai da shekara guda da ya yi a kan karagar mulki, Air Marshal Abubakar ya ce yakin Rasha da Ukraine ya hana NAF samun kayyakin jiragen sama da kuma kula da jirage masu saukar ungulu na Mi-series wadanda ke da matukar muhimmanci a ayyukanta na yaki da ta’addanci.

“Yayin da Nijeriya ke fuskantar kalubalen tsaro, kasar Amurka ta ba da goyon baya wajen sayen jiragen sama da makamantansu domin yaki da ta’addanci. Hakazalika, sojojin saman Nijeriya sun samu jiragen sama da alburusai daga kasashen China da Rasha kuma suna ci gaba da yin hadin gwiwa a fannin soji. Daidaita wadannan alakoki na da matukar muhimmanci ga muradun tsaron Nijeriya”.

Ya kara da cewa harin da Hamas ta kai kan Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba 2023 da kuma hare-haren da ‘yan tawayen Houthi ke kaiwa kan layukan jiragen ruwa ta tekun Bahar Maliya sun kuma yi “mummunan tasiri wajen samun fasahohin zamani da ake yayi kamar jiragen sama marasa matuka, da sadarwar tauraron dan adam da kuma kirkirarriyar basira ta AI.”

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Ya kuma kara da cewa karuwar juyin mulki da kuma ficewar kasashen Burkina Faso da Mali da Nijar daga kungiyar ECOWAS na da mummunar tasiri ga tsarin tsaro na yankin bai-daya a tsakanin Nijeriya da kasashen.

Ya yi nuni da cewa, hukumomin sojan kasar sun koma kasar Rasha domin neman taimakon tsaro, sakamakon gazawar kungiyar ECOWAS wajen magance tashe-tashen hankulan masu ikirarin jihadi a kasashen. .

“Bugu da kari, janyewar dakarun Majalisar Dinkin Duniya daga MINUSMA, da sojojin Chadi 2000 daga Mali, da kuma sojojin Jamhuriyar Nijar daga cikin rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa, na iya kara tsananta kalubalen tsaro a yankin Sahel, lamarin da ya haifar da kwararar makamai da ‘yan ta’adda. A ko da yaushe, wannan lamarin yana kawo cikas ga kokarinmu na yaki da ta’addanci.”

Ya yi gargadin cewa, “Saboda haka, da alama za mu shaida karuwar irin barazanar da aka fuskanta a baya. Don haka, ba wani riba ba ne, dole ne mu himmatu tare da kara himma wajen cimma burin gwamnatin Tarayya da ‘yan Nijeriya na samun wani mataki da zai kai mu ga samun nasara.

Sai dai kuma ya bayyana cewa NAF a cikin watanni 12 da suka gabata ta samu gagarumin ci gaba wajen yaki da ta’addanci, da ‘yan fashi, da masu satar mai da sauran ayyukan miyagun laifuka a kasar nan.

“Duk da haka, akwai sauran abubuwa da yawa da za a yi. Halin da ake ciki na matsin tattalin arziki – yawan rashin aikin yi na matasa, karuwar hauhawar farashin kayayyaki da kuma yawan talauci sun kara dagula yanayin tsaro a kasar. Don haka, dole ne mu yi wannan taron don samun nasara duba da yadda muka gudanar da ayyukanmu a cikin watanni 12 da suka gabata wajen kawo sauyi ga rundunar sojin saman Nijeriya domin biyan bukatun tsaron Nijeriya yadda ya kamata,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Air Marshal Hasan AbubakarNijeriyaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

Next Post

Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

20 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba - Hon. Lawal

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.