• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ke Dagula Rashin Tsaron Nijeriya – Babban Hafsan Sojin Sama

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Abin Da Ke Dagula Rashin Tsaron Nijeriya – Babban Hafsan Sojin Sama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban hafsan hafsa sojin sama, Air Marshal Hasan Abubakar ya danganta fafatawar da ake yi a tsakanin kasashen Amurka, Rasha da China a nahiyar Afirka, da kuma janyewar sojojin Jamhuriyar Nijar daga cikin rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa, a matsayin lamarin da ya kara ta’azzara kalubalen tsaro a yankin Sahel wanda ya haifar da kwararar makamai da ‘yan ta’adda zuwa Nijeriya.

Air Marshal Abubakar ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata ganawa da hafsoshin reshe da kwamandojin rundunar sojin sama da daraktoci da kuma daukacin manyan jami’an rundunar sojin saman Nijeriya a Abuja.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Sin Na Goyon Bayan Kokarin Kasashen Afrika Na Magance Matsaloli Ta Hanyar Da Suka Zaba

Da yake jawabi a wajen taron wanda ya zo daidai da shekara guda da ya yi a kan karagar mulki, Air Marshal Abubakar ya ce yakin Rasha da Ukraine ya hana NAF samun kayyakin jiragen sama da kuma kula da jirage masu saukar ungulu na Mi-series wadanda ke da matukar muhimmanci a ayyukanta na yaki da ta’addanci.

“Yayin da Nijeriya ke fuskantar kalubalen tsaro, kasar Amurka ta ba da goyon baya wajen sayen jiragen sama da makamantansu domin yaki da ta’addanci. Hakazalika, sojojin saman Nijeriya sun samu jiragen sama da alburusai daga kasashen China da Rasha kuma suna ci gaba da yin hadin gwiwa a fannin soji. Daidaita wadannan alakoki na da matukar muhimmanci ga muradun tsaron Nijeriya”.

Ya kara da cewa harin da Hamas ta kai kan Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba 2023 da kuma hare-haren da ‘yan tawayen Houthi ke kaiwa kan layukan jiragen ruwa ta tekun Bahar Maliya sun kuma yi “mummunan tasiri wajen samun fasahohin zamani da ake yayi kamar jiragen sama marasa matuka, da sadarwar tauraron dan adam da kuma kirkirarriyar basira ta AI.”

Labarai Masu Nasaba

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Ya kuma kara da cewa karuwar juyin mulki da kuma ficewar kasashen Burkina Faso da Mali da Nijar daga kungiyar ECOWAS na da mummunar tasiri ga tsarin tsaro na yankin bai-daya a tsakanin Nijeriya da kasashen.

Ya yi nuni da cewa, hukumomin sojan kasar sun koma kasar Rasha domin neman taimakon tsaro, sakamakon gazawar kungiyar ECOWAS wajen magance tashe-tashen hankulan masu ikirarin jihadi a kasashen. .

“Bugu da kari, janyewar dakarun Majalisar Dinkin Duniya daga MINUSMA, da sojojin Chadi 2000 daga Mali, da kuma sojojin Jamhuriyar Nijar daga cikin rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa, na iya kara tsananta kalubalen tsaro a yankin Sahel, lamarin da ya haifar da kwararar makamai da ‘yan ta’adda. A ko da yaushe, wannan lamarin yana kawo cikas ga kokarinmu na yaki da ta’addanci.”

Ya yi gargadin cewa, “Saboda haka, da alama za mu shaida karuwar irin barazanar da aka fuskanta a baya. Don haka, ba wani riba ba ne, dole ne mu himmatu tare da kara himma wajen cimma burin gwamnatin Tarayya da ‘yan Nijeriya na samun wani mataki da zai kai mu ga samun nasara.

Sai dai kuma ya bayyana cewa NAF a cikin watanni 12 da suka gabata ta samu gagarumin ci gaba wajen yaki da ta’addanci, da ‘yan fashi, da masu satar mai da sauran ayyukan miyagun laifuka a kasar nan.

“Duk da haka, akwai sauran abubuwa da yawa da za a yi. Halin da ake ciki na matsin tattalin arziki – yawan rashin aikin yi na matasa, karuwar hauhawar farashin kayayyaki da kuma yawan talauci sun kara dagula yanayin tsaro a kasar. Don haka, dole ne mu yi wannan taron don samun nasara duba da yadda muka gudanar da ayyukanmu a cikin watanni 12 da suka gabata wajen kawo sauyi ga rundunar sojin saman Nijeriya domin biyan bukatun tsaron Nijeriya yadda ya kamata,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Air Marshal Hasan AbubakarNijeriyaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Garambawul Da Muke Wa Tsarin Aikin Sojojin Nijeriya –Janar Musa

Next Post

Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Related

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

2 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

3 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

17 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

20 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

24 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

1 day ago
Next Post
Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba - Hon. Lawal

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.