ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ke Dagula Rashin Tsaron Nijeriya – Babban Hafsan Sojin Sama

by Leadership Hausa
2 years ago
Tsaron

Babban hafsan hafsa sojin sama, Air Marshal Hasan Abubakar ya danganta fafatawar da ake yi a tsakanin kasashen Amurka, Rasha da China a nahiyar Afirka, da kuma janyewar sojojin Jamhuriyar Nijar daga cikin rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa, a matsayin lamarin da ya kara ta’azzara kalubalen tsaro a yankin Sahel wanda ya haifar da kwararar makamai da ‘yan ta’adda zuwa Nijeriya.

Air Marshal Abubakar ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata ganawa da hafsoshin reshe da kwamandojin rundunar sojin sama da daraktoci da kuma daukacin manyan jami’an rundunar sojin saman Nijeriya a Abuja.

  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Kan Matsayin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam
  • Sin Na Goyon Bayan Kokarin Kasashen Afrika Na Magance Matsaloli Ta Hanyar Da Suka Zaba

Da yake jawabi a wajen taron wanda ya zo daidai da shekara guda da ya yi a kan karagar mulki, Air Marshal Abubakar ya ce yakin Rasha da Ukraine ya hana NAF samun kayyakin jiragen sama da kuma kula da jirage masu saukar ungulu na Mi-series wadanda ke da matukar muhimmanci a ayyukanta na yaki da ta’addanci.

ADVERTISEMENT

“Yayin da Nijeriya ke fuskantar kalubalen tsaro, kasar Amurka ta ba da goyon baya wajen sayen jiragen sama da makamantansu domin yaki da ta’addanci. Hakazalika, sojojin saman Nijeriya sun samu jiragen sama da alburusai daga kasashen China da Rasha kuma suna ci gaba da yin hadin gwiwa a fannin soji. Daidaita wadannan alakoki na da matukar muhimmanci ga muradun tsaron Nijeriya”.

Ya kara da cewa harin da Hamas ta kai kan Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba 2023 da kuma hare-haren da ‘yan tawayen Houthi ke kaiwa kan layukan jiragen ruwa ta tekun Bahar Maliya sun kuma yi “mummunan tasiri wajen samun fasahohin zamani da ake yayi kamar jiragen sama marasa matuka, da sadarwar tauraron dan adam da kuma kirkirarriyar basira ta AI.”

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

Ya kuma kara da cewa karuwar juyin mulki da kuma ficewar kasashen Burkina Faso da Mali da Nijar daga kungiyar ECOWAS na da mummunar tasiri ga tsarin tsaro na yankin bai-daya a tsakanin Nijeriya da kasashen.

Ya yi nuni da cewa, hukumomin sojan kasar sun koma kasar Rasha domin neman taimakon tsaro, sakamakon gazawar kungiyar ECOWAS wajen magance tashe-tashen hankulan masu ikirarin jihadi a kasashen. .

“Bugu da kari, janyewar dakarun Majalisar Dinkin Duniya daga MINUSMA, da sojojin Chadi 2000 daga Mali, da kuma sojojin Jamhuriyar Nijar daga cikin rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa, na iya kara tsananta kalubalen tsaro a yankin Sahel, lamarin da ya haifar da kwararar makamai da ‘yan ta’adda. A ko da yaushe, wannan lamarin yana kawo cikas ga kokarinmu na yaki da ta’addanci.”

Ya yi gargadin cewa, “Saboda haka, da alama za mu shaida karuwar irin barazanar da aka fuskanta a baya. Don haka, ba wani riba ba ne, dole ne mu himmatu tare da kara himma wajen cimma burin gwamnatin Tarayya da ‘yan Nijeriya na samun wani mataki da zai kai mu ga samun nasara.

Sai dai kuma ya bayyana cewa NAF a cikin watanni 12 da suka gabata ta samu gagarumin ci gaba wajen yaki da ta’addanci, da ‘yan fashi, da masu satar mai da sauran ayyukan miyagun laifuka a kasar nan.

“Duk da haka, akwai sauran abubuwa da yawa da za a yi. Halin da ake ciki na matsin tattalin arziki – yawan rashin aikin yi na matasa, karuwar hauhawar farashin kayayyaki da kuma yawan talauci sun kara dagula yanayin tsaro a kasar. Don haka, dole ne mu yi wannan taron don samun nasara duba da yadda muka gudanar da ayyukanmu a cikin watanni 12 da suka gabata wajen kawo sauyi ga rundunar sojin saman Nijeriya domin biyan bukatun tsaron Nijeriya yadda ya kamata,” in ji shi.

Tsaron
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Next Post
Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba - Hon. Lawal

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.