• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Taro Ya Nuna Cewa Afirka Na Da Wani Sahihin Aboki

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Wannan Taro Ya Nuna Cewa Afirka Na Da Wani Sahihin Aboki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ta yaya za a gane ko wani mutum yana da gaskiya? Ta hanyar gaya masa bukatarka, sa’an nan a duba yadda zai mayar maka da martani. Zai nuna yanayin ko-in-kula, ko kuma zai yi kokarin ba ka amsa mai gamsarwa.

 

A ranar 12 ga wata, kasar Saliyo, bisa matsayinta na kasar dake shugabantar kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya na karba karba, ta shirya wani taron muhawara, don tattauna batun kara kujerun kasashen Afirka cikin kwamitin sulhun.

  • Xi Ya Yabawa ‘Yan Wasan Olympics Na Sin Da Suka Samarwa Kasar Daukaka 
  • Peng Liyuan Ta Gana Da Uwar Gidan Shugaban Vietnam

Yayin da yake jawabi, shugaban kasar Saliyo Julius Bio ya ce, har yanzu babu wata kujerar din-din-din ta nahiyar Afirka a kwamitin, kana babu isassun kujeru wadanda ba na din-din-din ba mallakar kasashen Afirka, lamarin da a cewarsa ya nuna rashin adalci irin na tarihi.

 

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

A nata bangare, Sithembile Mbete, wata masaniyar ilimin siyasa ta kasar Afirka ta Kudu, ita ma ta ba da jawabi wajen taron, inda ya yi karin tsokaci kan batun rashin adalci da kasashen Afirka ke fuskanta. A cewarta, asalin rashin adalcin shi ne cinikin bayi da kasashen yamma suka kwashe shekaru 400 suna yi, da yadda kasashen Turai da kasar Amurka suka kasa nahiyar Afirka zuwa yankunan mulkin mallaka daban daban, a wani taron da suka gudanar a birnin Berlin na kasar Jamus a shekarar 1884.

 

Abin lura shi ne, dangane da jawaban da wakilan kasashen Afirka suka yi, wadanda suka nuna rashin jin dadinsu, game da rashin adalci da aka yi musu, kasar Amurka ta nuna yanayin ko-in-kula, ko da yake ta taba halarta da cin moriyar cinikin bayi, gami da kasancewarsa a teburin tattaunawar taron Berlin na shekarar 1884. Yayin da wakiliyar kasar Amurka a MDD Linda Thomas-Greenfield ke ba da jawabi, ta ambaci maganar da shugaban kasarta Joseph Biden ya yi, ta “nuna goyon baya ga Afirka, da Latin Amurka, da kasashen Caribbeans kan batun neman kujerun din-din-din a kwamitin sulhun MDD” kadai, ba tare da tabo maganar rashin adalci da Afirka ke fuskanta ba, balle ma tuba kan laifukan da kasar Amurka ta taba aikatawa.

 

A dai wajen wannan taro, dangane da bukatar kasashen Afirka, ta yaya kasar Sin ta mayar da martani? A cikin jawabinsa, wakilin Sin a MDD Fu Cong ya nuna goyon baya ga nahiyar Afirka, inda ya yi Allah wadai da cin zarafin al’ummun nahiyar Afirka da kasashen yamma suka yi a tarihi, da bayyana matakan da suka dauka a matsayin asalin rashin adalci dake damun kasashen Afirka. Kana ya ce har yanzu wannan yanayi na rashin adalci na ci gaba, ganin yadda wasu kasashen yamma ke tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, da neman cin zarafi da sarrafa su.

 

Daga baya, Fu Cong ya ba da shawara kan matakan da ya kamata a dauka, don daidaita yanayin rashin adalci dake damun kasahen Afirka. A cewarsa, da farko, ya kamata kasashen yamma su daina tsoma baki cikin harkokin gidan kasashen Afirka, da mayar wa jama’ar kasashen Afirka cikakken ikon kula da kai, da tabbatar da makomar kai.

 

Na biyu, a taimaki kasashen Afirka a kokarinsu na samun ci gaba mai dorewa, da raya masana’antu, da zamanantarwa.

 

Na uku, a tabbatar da samun dimbin bangarori masu fada a ji a duniya, da nuna cikakken goyon baya ga kasashen Afirka, kan bukatarsu ta yin gyare-gyare kan tsarin kwamitin sulhun MDD.

 

Kana na hudu, a gyara tsarin hada-hadar kudi ta duniya, don samar da karin tallafi ga kasashen Afirka, da kawo karshen matakin wasu kasashe na yin amfani da manufar kudin su wajen kwace dukiyoyin da jama’ar kasashen Afirka suka tattara.

 

A zahiri kasar Sin tana goyon bayan kasashen Afirka, har ma ta samar da shawarwari masu amfani. Idan ka san manufofin kasar Sin, to, za ka gane duk wadannan shawarwari na cikin manufofin kasar na dogon lokaci.

 

Idan mun kalli taron kwamitin sulhun MDD da ya gudana a matsayin wata jarrabawa kan cewar “ko ana nuna gaskiya da sahihanci ga kasashen Afirka”, to, na san kasar Sin ta ci jarrabawar. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Gana Da Shugabannin Majalisun Dokokin Kasashen Duniya

Next Post

Gwamnatin Sokoto Za Ta Sayar da Tireloli 300 Na Shinkafa A Farashi Mai Rahusa

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

5 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

1 week ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

2 weeks ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 weeks ago
Next Post

Gwamnatin Sokoto Za Ta Sayar da Tireloli 300 Na Shinkafa A Farashi Mai Rahusa

LABARAI MASU NASABA

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.