• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kakar Da Ta Fi Dacewa Da Noman Wake A Nijeriya

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Kakar Da Ta Fi Dacewa Da Noman Wake A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wake na daya daga cikin cimar akasarin ‘yan Nijeriya, duba da cewa yana daya daga cikin abinci mai gina jikin Dan’adam. Wannan dalili ne ya sa a kauyuka da birane al’umma da dama ke noman sa, domin amfanin gida da kuma sayarwa a kasuwanni.

Sai dai, wasu manoman ba sa bin hanyar da ta dace wajen noman wannan Wake. Domin kuwa, a Nijeriya girbin da ake samu har yanzu bai wuce kasa da tan 0.2 a kowace hekta daya, duk da cewa kuma; masu yin nomana Waken ta hanyar da ta dace, sukan iya girbe kimanin tan 2 a kowace hekta guda.

Watannin da suka fi dacewa a noma Wake a kasar nan, na farawa ne daga watan Mayu zuwa na Yuni.

Kazalika, dangane da yanayin kakar damina; ana kuma yin nomansa daga watan Mayu, Yuni da kuma na Yuli.

Babu shakka, nomansa a cikin wadannan watanni; zai sa ya samu isasshe ko kuma wadataccen ruwa.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Haka zalika, wadanda ke noman wannan Wake a lokacin rani; za su iya shuka Irinsa a kowane irin lokaci.

Watannin da suka fi dacewa a shuka Wake a Nijeriya sun hada da watan Afirilu, Mayu, Yuni, Juli, Augusta, Satumba har kuma zuwa Disamba.

 

Watan Afirilu:

A kudancin Nijeriya, ana fara shuka Irin Wake a watan Afirilu, sakamakon cewa a wannan wata ne ake fara yin ruwan sama.

Har ila yau, a cikin watan ne kuma Irin Waken da aka shuka; galibi ba a cika samun wata matsala kamar ta kwarin da ke lalata amfanin gona ko wani abu makamancin haka ba.

 

Watan Mayu:

A Nijeriya, musamman a yankunan da suke da dausayi ne ake fara samun ruwan sama, wanda hakan ya sa watan ya kasance, lokacin da ya fi dacewa a shuka Irin Waken.
Kazalika, a cikin watan ne Waken da aka shuka zai yi girma sosai; domin ba a cika samun kwarin da suke lalalata amfanin gonar ba.

 

Watan Yuni:

Shi ma wannan watan, na daya daga cikin watan da ya dace a shuka Irin Wake a kudancin Nijeriya da kuma Arewacin kasar. Domin kuwa, a cikin watan ba a cika samun kwarin da ke lalata amfanin gonar ba.

 

Watan Yuli:

Shi ma wannan watan, na daya daga cikin watannin da suka dace a noma Wake, musamman a kudancin wannan kasa, a kuma cikin watan; ba a cika samun kwarin da ke lalata amfanin ba.

Watan Augusta:

Musamman a kudancin Nijeriya, wannan watan na da matukar kyau a shuka Irin Wake, sai dai ana kuma bukatar manomi ya kasance ya tanadi kayan ban ruwan da zai yi wa Waken.

Haka nan, a Arewacin Nijeriyar; ganin cewa a watan ne ake samun ruwan sama mai yawa, watan ya kasance mafi kyau na shuka Irin Waken.

 

Watannin Satumba zuwa na Disamba:
Zai iya yiwuwa, Wake ya girma a cikin wadannan watanni har zuwa cikin watan Oktoba.

Daga watan Satumba zuwa Disamba, nan ne kakar rani ke fara kunnu kai; inda kuma za a iya samun bullar kwarin da ke lalata amfanin gona, wanda a cikin watannin ne kuma ake so manomi ya rika amfani da magungunan kashe kwari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Manoman shinkafaNoman Ridi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samar Da Naira Biliyan 2.5 Don Bunkasa Ma’adanai A Nijeriya

Next Post

Takaitaccen Nazari A Kan Noman Nau’o’in Abinci 7

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

6 days ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

6 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Waiwaye Game Da Shirin “Kauyuka Dubu Goma” Da Daidaita Yanayin Kauyukan Kasar Sin

Takaitaccen Nazari A Kan Noman Nau’o’in Abinci 7

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.