• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaitaccen Nazari A Kan Noman Nau’o’in Abinci 7

by Abubakar Abba and Sulaiman
11 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Waiwaye Game Da Shirin “Kauyuka Dubu Goma” Da Daidaita Yanayin Kauyukan Kasar Sin

•Yadda manoma suke aiki a cikin gonakin kauyen Cailu

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Allah ya albarkanci Nijeriya da lokuta biyu na yin noma, wato lokacin rani da kuma damina; wanda a lokacin damina kamar yadda aka saba, ana fara samun ruwan sama ne daga watan Afrilu zuwa na Oktoba.

 

Hakan, na bai wa manoma damar yin shuka tare da girbe nau’ikan amfanin gonan da suka shuka.

  • An Samar Da Naira Biliyan 2.5 Don Bunkasa Ma’adanai A Nijeriya
  • Zaben Shugabanni: Sabon Rikici Ya Kunno Kai A PDP

Manyan amfanin gonar da aka fi nomawa a kakar damina sun hada da; Masara, Shinkafa, Kubewa, Kankana, Tumatir, Tattasai da kuma Rogo.

 

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1- Masara: Ta kasance daya daga cikin manyan amfanin gona a Nijeriya da ake nomawa a lokacin rani, wadda kuma ake sarrafawa zuwa nau’ikan abinci daban-daban.

Ya fi kyau a shuka Irinta daga watan Afirilu zuwa na Mayu, duba da cewa lokacin ne a ake fara samun mamakon ruwan sama.

Yana da kyau a sani cewa, Masara na bukatar ingantacciyar kasar noma mai kyau tare da danshi mai yawa; sannan dole ne a kula da cire mata Ciyawa, domin ta samu ta girma cikin sauri.

2- Shinkafa: Ita ma na daya daga cikin manyan amfanin gona a Nijeriya, wadda ake shuka Irinta da damina; ana kuma sarrafa nau’ikan abinci ir-iri da ita. Kazalika, ya fi dacewa a shuka Irinta daga watan Afrilu zuwa na Yuli, musamman ganin cewa; a lokacin ne ake samun ruwan sama mai yawan gaske.

Haka zalika, Shinkafa na bukatar a yi mata gyaran gona kafin a shuka Irinta tare da cire mata Ciyawa, don ta samu damar girma da sauri.

3- Kubewa: Ita ma na daya daga cikin kayan lambun da ake nomawa da damina, sannan kuma tana dauke da sinadarin da ke gina jikin Dan’adam.

Kazalika, ta fi dacewa a shuka Irinta daga watan Afrilu zuwa na Yuli; duba da cewa a cikin wadannan watanni ne aka fi samun mamakon ruwan sama.

Har wa yau kuma, tana bukatar kasar noma mai kyau tare da yawan cire mata Ciyawa; don a samu ta yi girma da wuri.

4 Kankana: Ita ma a Nijeriya, ana bukatar a shuka Irinta a lokacin damina; kamar yadda aka sani ne kuma tana dauke da sinadarin da ke gina jikin Dan’adam, ana kuma sarrafa ta zuwa nau’ika daban-daban.

Akasari, an fi shuka Irinta ne daga watan Afrilu zuwa na Mayu; sannan kuma ana bukatar a yi mata gyaran gona kafin a shuka Irinta tare da cire mata Ciyawa, don ta girma da wuri.

5- Tumatir: Yana daya daga cikin kayan lambu da ake shuka Irinsa a Nijeriya a lokacin damina, wanda kuma ya fi kyau a shuka Irinsa daga watan Afrilu zuwa na Mayu tare kuma da shuka Irinsa a kasar noma mai kyau da cira masa Ciyawa, don a samu ya girma da wuri.

6- Tattasai: Shi ma ya kasance daya daga cikin kayan lambun da ake shuka Irinsa a Nijeriya, musamman a lokacin damnina. An fi so a shuka Irinsa daga watan Afrilu zuwa na Mayu, kazalika kuma yana bukatar kasar noma mai kyau tare da danshi, sannan dole a kula da cire masa Ciyawa, domin ya girma da wuri.

7- Rogo: Shi ma ana shuka Irinsa a Nijeriya a lokacin damnina, sannan kuma ana sarrafa shi zuwa nau’ikan abinci daban-daban.

Mafi akasari, an fi bukatar a shuka Irinsa daga watan Afrilu zuwa na Yuni, kana kuma yana bukatar ingantacciyar kasar noma da kuma waje mai matukar danshi, don ya girma da wuri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kakar Da Ta Fi Dacewa Da Noman Wake A Nijeriya

Next Post

An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe

Related

Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

7 days ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

7 days ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

3 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe

An Ceto Ɗalibai 20 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Binuwe

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.