ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Wata Mata A Gaban Kuliya Bisa Zargin Damfarar Wani Kamfani N350m

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
1 year ago
Kotu

Rundunar ‘yansandan Jihar Legas, a ranar Talata, ta gurfanar da wata mata mai suna Rukayya Dantata ‘yar shekaru 35 a gaban kuliya bisa zargin damfarar wani kamfanin tuntuba na Bureau de Change kudi Naira miliyan 350,900,000.

 

An gurfanar da Dantata a gaban kotun laifuffuka ta musamman da ke Ikeja da laifuffuka biyu da suka hada da zamba, damfara da kuma karbar kudi ta hanyar karya.

ADVERTISEMENT
  • EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Taraba Ishaku Kan Zargin Badaƙalar 27bn
  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

Lauyan mai shigar da kara, Ezekiel Rimamsomte, ya shaida wa kotun cewa Dantata ta aikata laifukan da ake zarginsa tsakanin watan Yuli zuwa Agustan 2022.
Ya ce wacce ake kara ta samu Naira miliyan 350,900,000 ta hanyar damfara, inda aka tura ta zuwa asusunta na Zenith Bank, 2082551256, da kuma asusun kamfaninta mai suna Adat Bentures’ mai lamba, 1014937041, da sunan Rukayya Saadina Dantata.

Rimamsomte ta kara da cewa Dantata ta yaudari wadanda masu kudin, Saka Rasak na Rosiyike, da wasu na kamafanin Financial Consultant Ltd, da ke No. 50 Kingsway Building, Legas, ta hanyar yin kamar suna gudanar da harkokin kasuwanci na halal.
A cewarta, laifukan da aka aikata sun ci karo da sashe na 1 (a) (3) na dokar damfara da sauran laifukan da suka shafi doka ta 2006, da sashe na 323 na dokar laifuka ta Jihar Legas 2015.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sai dai Dantata ya musanta zargin da ake mata.

Igbodo ya bukaci kotun da ta bayar da belin wacce ake tuhuma a karkashin “mafi sassaucin sharuda,” yana mai cewa, “Wanda ake tuhumar ya bi dukkan sammacin ‘yansanda da Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arziki Ta’annati, kuma ba ta tsallake beli ba, duk da kalubalen lafiyarta.”

Ya kuma shaida wa kotun cewa mijin Dantata, Alhaji Ismaih Singer, da kuma wata Otunba Olutaye Ariyo sun hallara a gaban kotu domin a ba ta belinta.

Mai gabatar da kara bai musanta da neman belin ba kuma ya bar hukuncin ga hukuncin kotun.

A wani takaitaccen hukunci mai shari’a Rahmon Oshodi ya bayar da belin Dantata kan kudi Naira miliyan 30 tare da mutane biyu da za su tsaya mata.

Alkalin ya bayyana cewa, “Dukkanin wadanda za su tsaya mata dole ne su ba da takardar shaidar biyan haraji na shekaru uku ga gwamnatin Jihar Legas.”

Mai shari’a Oshodi ya kuma umurci Dantata da ta ajiye fasfo dinta da sauran takardun tafiya zuwa ga babban magatakardar kotun, inda ya kara da cewa dole ne magatakardar ta tantance adireshin gidanta da ofishinta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Next Post
Xi Ya Yi Kira Ga Ma’aikatan Masana’antu Da Su Ba Da Gudummawar Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Ma’aikatan Masana’antu Da Su Ba Da Gudummawar Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.