• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

by Abubakar Abba
11 months ago
in Labarai
0
Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan an gano danyen mai a 1950 Nijeria ne, aka fara yiwa fannin aikin noma na Nijeriya rkon Sakanr Kashi.

Fannin wanda na daya daga cikin gwagwarmayar da masu hakilon samun yancin kan kasar suka karfafa shi na kan gaba wajen habaka tattalin arzikin kasar.

  • Nazari Kan Gazawar Tsofaffin Ministocin Noma 52 Da Suka Shude A Nijeriya
  • Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

Kafin samun ‘yancin kan kasar, a 1950 Nijeriya ce kan gaba a duniya, wajen noma Kwakwar Manja da kuma Cocoa.

Hakazalika, fannin na samar da ayyukan yi da suka kai sama da kashi 70, wanda hakan ya kai kusan kashi 62.3 na kudaden musayar na shiga, da kasar ke samu.

Bisa wata kididdiga da aka samu daga gun bankin duniya ta nuna cewa, fanin na samar da sama da kashi 60, ga tattalin arzikin kasar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Sai dai, bayan gano danyen man a 1950, hakan ya janyo an yi watsi da fannin, wanda hakan ya sanya kimar Nijeiya a fannin aikin noma a fadin duniya, ta fadi warwas.

Amma domin a sake farfado da kimar Nijeriya a fannin, shugabannin da suka mulki kasar, sun kirkiro da tsare-tsaren aikin noma da ban da ban.

Sai dai, abun takaicin shi ne, wadannan tsare-tsaren, kusan za a iya cewa, ba su wani tasiri ba saboda sauye-sauyen shugabanci da aka samu a kasar.

 

Tsare-Tsaren Da Aka Kirkiro Bayan Samun ‘Yancin Kai:

Domin rage radadin yakin basasa a fanin aikin noma, tsohuwar gwamnatin mulkin soji ta Janar Yakubu Gowon mai murabus, ya kirkiro da tsarin NAFPP na kasa a 1972 don bunkasa samar da abinci, ta hanyar ilimantar da manoma.

An kaddamar da tsarin na gwaji a jihohin Anambra, Imo, Ondo, Oyo, Ogun, Benue, Filato da Kano.

Sai dai, tsarin ya ci karo da kalubale na rashin gazawar manoma na kafa kungiyoyi don a tallafa masu da kudaden aikin noma da sauran kayan aiki.

Hakazalika,a a 1973, Gowon ya kafa hukumar RBDA bisa nufin samar da kayan aikin noma rani, ta hanyar kakkafa Dam Dam don tara ruwan na noman rani.

Daga baya kuma a 1975ya kirkiro da aikin bunkasa aikin na noma ADP.

Bugu da kari, a lokacin tsohowar gwamnatin mulkin soji ta Cif Olusegun Obasanjo a 1976 bankin CBN, ya kirkiro da aikin habaka aikin noma na kasa OFN.

Manufar ita ce, don a kara yawan noma da ake yi a kasar, musamman don a samar da abinci, mai gina jiki.

Tsarin ya kai har 1979 na lokacin mulikin tsohowar gwamnatin farar hula ta marigayi Shehu Shagari.

A watan Afirilun 1980, Shagari ya kirkiro da tsarin farfado da aikin noma na GRP bisa nufin samar da wadataccen abinci ta hanyar yin amfani da fasahar zamani.

Bugu da kari, a 1986, lokacin tsohuwar mulkin soji ta tsohon shugaban kasa na mulkin soji Janar Ibrahim Badamasi Babangida mai murabus, ya kirkiro da tsarin DFRRI, bisa nufin tallafa wa alumomi.

 

Daga 1999 zuwa 2020:

Tsohohuwar gwamnatin farar hula ta tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo, a watan Afirilun 2003, ya kirkiro da tsarin aikin samar da wadataccen abinci na kasa NSPFS.

Ya kirkiro da tsarin don a taimaka wa manoma su samun karin kudaden shiga da karfafa ayyukan noman rani da sauransu.

Sai dai, tsarin ya ci karo da matsala saboda manoman da aka bai wa kudin rancen yin noma, sunki maido da kuadaden a kan lokaci tare da kuma kalubalen da manoman suka fuskanta na rashin yin amfani da kimiyyar fasahar noma.

A shekaru takwas na mulkin Obasanjo, fannin ya bayar da gudunamawa na bunkasa tattalin arzikin kasar.

Har ila yau, a lokacin tsohuwar mulkin marigayi shugaban kasa Umaru Yar’Adua, ya kirkiro da tsarin ajanda bakwai da kuma shirin habaka aikin noma na kasa NFSP.

Manufar shirin ya hada da; bayar da kudaden hadaka na aikin noma na FADAMA III; IFAD da ayyuan bunkasa aikin noma na ADB da sauransu.

Yar’Adua, ya bayar da gagarumar gudunmawa ga tattalin arzikin kasar wadda ta kai kashi 25.31.

Bugu da kari, a 2011, tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya kaddamar da tsarin aikin noma na ATA.

Ya kirkiro da tsarin ne, domin a habaka noman, musamman kanaanan manoma wanda kimanin kanannan manoma 45,300 da ke a karkara suka amfana.

A lokacin, fannin ya taimaka da wajen kashi 21.09 ga tattalin arzikin kasar.

Hakazalika, a lokacin mulkin tsohuwar gwamnatin tsohon shugaban kasa na mulkin dimokiradayya Muhammadu Buhari a shekarar 2015, ya kirkiro da tsarin habaka aikin noma na APP.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarmingNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

Next Post

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Related

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

15 minutes ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

42 minutes ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

2 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

4 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

7 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

7 hours ago
Next Post
Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.