• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zargin Horo Da Ruwan Zafi Ya Jefa Rayuwar Budurwa Cikin Larura

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2, Sun Kwato Makamai A Anambra
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan uwan wata budurwa ‘yar shekara 23 mai suna Nana Fiddausi Sa’idu da ke da zama a Unguwar Makera gudunmar Rigasa a Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna, sun yi kira ga masu hannu da shuni, da su taimaka wa rayuwar buduwar, biyo bayan kamuwa da wata larura wanda hakan ya janyo halitta ta koma tamkar, ta karamar yarinya.

Wata kanwar mahaifiyarta mai suna A’i ta yi zargin cewa, Nana ta kamu da larurar ce, bayan da mahaifin Nana ya dauke ta daga gun dangin mahaifiyar ta ya kuma ya mayar da ita ga wata ‘yaruwarsa da ke a Jihar Kano.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Ta ce, lafiyar ta lau mahaifinta ya dauke ta daga wurinsu amma sai ta gudo daga gun ‘yaruwar ta sa daga Kano saboda ‘yar uwar uban, na yi mata mata horo da ruwan zafi.

A cewarta, Nana ta je tashar mota ta Kano ne, inda ta nemi taimakon mutane da su sanya a mota ta dawo Kadauna, suka dauko ta suka kawo ta gidanmu.

Ta ce, bayan da Nana ta kamu da larurar babu wata kulawa daga mahaifinta, ya yi wasti da ita, kuma ‘yanu wansa babu wanda ya damu da halin da take a ciki.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Ta ce, bayan kwana biyu ta fadi aka kaita asibitin Nasiha ba a cikin hayyacinta ba, aka kwantar da ita, a rika kiran mahaifinta a waya, daga baya ya zo ya iske, ana yi mata karin ruwa, sai ya cire robar karin ruwan har suka fara sa-insa da wata jami’ar asibitin, amma ya matsa sai da aka cire mata aka dawo da ita gida.

Ai ta ce, larurar ta koma mata kamar farfadiya, wanda duk inda take, sai ta fadi tana fisge-fisge, yanzu gashi mahaifinta ya rasu, kuma ‘yanuwansa, babu wanda ya damu da halin laruwar da take ciki.

Da aka tambaye ta ko sun sanar da hukuma lamarin ta ce, ba a sanar da hukuma ba, inda ta ce, tun ana yi mata magani, yanzu dai karfinsu ya kare, amma suna neman taimako don a ceto raywarta.

Shi ma Ibrahim Hannafi wanda yayan mahaifiyar Nana ne, ya zargi ‘yan uwan mahaifi da nuna halin ko in kula a kan larurar Nana, inda ya yi kira ga masu hali, da su taimaka a ceto raywar budurwar.

Ya ce, lokacin mahaifinsu yana raye, shi ne yake kulawa da halin da take ciki amma ya ce, mu kyale, ‘yan uwan mahaifinta da halin sun nuna ko in kula dangane da larurar ta, kuma bai bar su mun dauki wani mataki ba a lokacin da yake raye.

Shi kuwa Malam Anas Musa dan kungiyar kare hakkin ‘yan’Adam cewa ya yi, an zalunci yarinyar, duba da yadda dangin mahaifinta suka yi watsi da ita, suka bar nauyinta a gun dangin uwarta, inda ya ce, a kungiyance, za mu bi wa Nana kadin tauye mata ‘yancinta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BudurwaHoro
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Wata Mata Da Laifin Azabtar Da Yara Kanana A Adamawa

Next Post

Kotu Ta Garkame Wani Dan Shekara 43 Da Ya Lalata Agolarsa

Related

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

17 hours ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

18 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

1 week ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 month ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 month ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue

Kotu Ta Garkame Wani Dan Shekara 43 Da Ya Lalata Agolarsa

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.