ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zargin Horo Da Ruwan Zafi Ya Jefa Rayuwar Budurwa Cikin Larura

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Horo

‘Yan uwan wata budurwa ‘yar shekara 23 mai suna Nana Fiddausi Sa’idu da ke da zama a Unguwar Makera gudunmar Rigasa a Karamar Hukumar Igabi a Jihar Kaduna, sun yi kira ga masu hannu da shuni, da su taimaka wa rayuwar buduwar, biyo bayan kamuwa da wata larura wanda hakan ya janyo halitta ta koma tamkar, ta karamar yarinya.

Wata kanwar mahaifiyarta mai suna A’i ta yi zargin cewa, Nana ta kamu da larurar ce, bayan da mahaifin Nana ya dauke ta daga gun dangin mahaifiyar ta ya kuma ya mayar da ita ga wata ‘yaruwarsa da ke a Jihar Kano.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Ronaldo Da Messi Ne Kan Gaba A Jerin ‘Yan Wasan Da Suka Fi Karbar Albashi

Ta ce, lafiyar ta lau mahaifinta ya dauke ta daga wurinsu amma sai ta gudo daga gun ‘yaruwar ta sa daga Kano saboda ‘yar uwar uban, na yi mata mata horo da ruwan zafi.

ADVERTISEMENT

A cewarta, Nana ta je tashar mota ta Kano ne, inda ta nemi taimakon mutane da su sanya a mota ta dawo Kadauna, suka dauko ta suka kawo ta gidanmu.

Ta ce, bayan da Nana ta kamu da larurar babu wata kulawa daga mahaifinta, ya yi wasti da ita, kuma ‘yanu wansa babu wanda ya damu da halin da take a ciki.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Ta ce, bayan kwana biyu ta fadi aka kaita asibitin Nasiha ba a cikin hayyacinta ba, aka kwantar da ita, a rika kiran mahaifinta a waya, daga baya ya zo ya iske, ana yi mata karin ruwa, sai ya cire robar karin ruwan har suka fara sa-insa da wata jami’ar asibitin, amma ya matsa sai da aka cire mata aka dawo da ita gida.

Ai ta ce, larurar ta koma mata kamar farfadiya, wanda duk inda take, sai ta fadi tana fisge-fisge, yanzu gashi mahaifinta ya rasu, kuma ‘yanuwansa, babu wanda ya damu da halin laruwar da take ciki.

Da aka tambaye ta ko sun sanar da hukuma lamarin ta ce, ba a sanar da hukuma ba, inda ta ce, tun ana yi mata magani, yanzu dai karfinsu ya kare, amma suna neman taimako don a ceto raywarta.

Shi ma Ibrahim Hannafi wanda yayan mahaifiyar Nana ne, ya zargi ‘yan uwan mahaifi da nuna halin ko in kula a kan larurar Nana, inda ya yi kira ga masu hali, da su taimaka a ceto raywar budurwar.

Ya ce, lokacin mahaifinsu yana raye, shi ne yake kulawa da halin da take ciki amma ya ce, mu kyale, ‘yan uwan mahaifinta da halin sun nuna ko in kula dangane da larurar ta, kuma bai bar su mun dauki wani mataki ba a lokacin da yake raye.

Shi kuwa Malam Anas Musa dan kungiyar kare hakkin ‘yan’Adam cewa ya yi, an zalunci yarinyar, duba da yadda dangin mahaifinta suka yi watsi da ita, suka bar nauyinta a gun dangin uwarta, inda ya ce, a kungiyance, za mu bi wa Nana kadin tauye mata ‘yancinta.

Horo
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Tsohowar Shugaban Kotun Gargajiya A Benue

Kotu Ta Garkame Wani Dan Shekara 43 Da Ya Lalata Agolarsa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.