• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Dalilin Da Ya Sa ‘Yansanda Suka Kasa Kama Tsohon Gwamnan Kogi’

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Kogi

Fadar shugaban kasa ta yi karin haske game da wasan kwaikwayo da rudanin shari’a da ke tattare da gazawar jami’an tsaro wajen cafke Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, duk da kokarin da aka yi.

Mai Magana Da Yawun Shugaban Kasar, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan yayin da yake magana a wani shirin zamantakewa da tattalin arziki na gidan talabijin na Channels, mai suna ‘Inside Sources with Laolu Akande’.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Onanuga ya bayyana kalubale na musamman da ke tattare da kusancin Bello da magajinsa, Gwamna Usman Ododo, wanda ke da kariyar tsarin mulki.

LEADERSHIP ta tunatar da cewa, a watan Afrilu, Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta bayyana cewa ana neman Bello ne bisa zarginsa da aikata laifukan kudi da suka hada da Naira biliyan 80.2. Duk da cewa hukumar EFCC ta yi yunkurin cafke tsohon gwamnan, amma yunkurin ya ci tura, inda rahotanni suka ce Ododo ya kare Bello tare da ba wa gwamnan mafaka a masaukinsa.

Ya kara da cewa, yayin da hukumar EFCC ta dukufa wajen gurfanar da Bello a gaban kuliya, kariyar da aka bai wa Gwamna Ododo a karkashin tsarin mulki na dagula duk wani yunkuri na kama tsohon gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Ya ci gaba da cewa, “Wannan ita ce matsalar domin idan shi (Bello) ya zauna a gidan Gwamna Ododo, ‘yan sanda ba za su iya yin komai ba saboda za su keta wannan rigar da gwamna ke da ita.

“Kamar jami’in diflomasiyya ne da yake da kariya, don haka ba za ku iya yin komai game da shi ba. Kun tuna a Burtaniya lokacin da suke neman mutumin nan Wikileaks, sai ya je ya buya a wani ofishin jakadanci a Biritaniya, ba abin da su ( jami’an tsaro) za su iya yi, dole haka nan suka bar shi a can. Ina tsammanin daga baya ne ya fito suka kama shi,” Onanuga ya fadi haka yayin da yake tabbatar da rashin ikon EFCC.

Tsohon gwamnan Jihar Kogi, wanda ya yi mulki daga shekarar 2016 zuwa Mayu 2024, ya kasa gurfana a gaban kotu duk da yawan sammaci da kuma dage sauraren karar da aka yi masa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso

EFCC Ta Cafke Wadanda Suka Damfari Attajiri Aminu Dantata

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.