• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Fiye Da Biliyan 465 A Matsayin Kasafin Kuɗin 2025

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Fiye Da Biliyan 465 A Matsayin Kasafin Kuɗin 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a ranar Alhamis ya gabatar da kasafin kuɗin 2025 da yawansa ya kai Naira Biliyan 465,805,248,317.12 ga majalisar dokokin jihar Bauchi domin nazari da neman amincewa.

 

Da ya ke gabatar da kasafin, gwamnan ya jinjina wa irin haɗin kai da ake samu a tsakanin majalisar dokokin jihar da bangaren zartarwa na jihar wanda ya misalta hakan a matsayin hanyar ciyar da jihar gaba.

  • Kin Amincewa Da Kudurin Tsagaita Bude Wuta A Gaza Da Amurka Ta Yi Ya Kara Nuna Rashin Mutunci Da Adalcinta
  • Dole Ne Ƙungiyoyin Ƴan Banga Su Haɗa Kai – Kauran Yauri

A cewar Gwamnan, Naira biliyan 283.8 ne aka ware a matsayin hasashen kuɗin da za a kashe a ɓangaren manyan ayyuka wato kaso 60.7 cikin 100 na kasafin na shekarar baɗi.

 

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Yayin da kuma sauran kaso 39.3 aka ware domin gudanar da ayyukan yau da gobe. Sai ya nemi haɗin kan majalisar wajen ganin ta gudanar da ayyukan ta da wuri domin amincewa a kan lokaci, lamarin da zai taimaki gwamnatin wajen gudanar da ayyukan da aka tsara aiwatarwa a shekara mai zuwa.

 

Shi kuma a nasa ɓangaren bayan karɓar kundin kasafin, Kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi, Rt. Hon. Abubakar Y Sulaiman, ya yi alƙawarin cewa, mambobin majalisar za su bibiyi kundin kasafin a tsakanake domin hanzarin amincewa da shi.

 

Ya nemi rassa da hukumomin gwamnatin jihar da su mutunta gayyatar kwamitocin majalisar domin kare kasafin ma’aikatun su domin sauƙaƙa wa majalisar ayyukan nata don ganin an amince da kasafin a kan lokaci


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasafin KudiKundin Tsarin Mulki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kin Amincewa Da Kudurin Tsagaita Bude Wuta A Gaza Da Amurka Ta Yi Ya Kara Nuna Rashin Mutunci Da Adalcinta

Next Post

Wakilin Sin Ya Ce Abin Kunya Ne Hawa Kujerar Na Ki Da Amurka Ta Yi A Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

19 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

3 days ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Ce Abin Kunya Ne Hawa Kujerar Na Ki Da Amurka Ta Yi A Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza

Wakilin Sin Ya Ce Abin Kunya Ne Hawa Kujerar Na Ki Da Amurka Ta Yi A Kan Kudurin Tsagaita Wuta A Gaza

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.