• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Tabbaci Ga Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Tabbaci Ga Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karshen shekara lokaci ne na waiwaye adon tafiya. Sai dai a wannan shekarar da muke ciki, mun gane ma idanunmu dimbin abubuwan takaici da suka abku a duniya. Wani abu da zai iya sanyaya zuciyarmu shi ne, yadda huldar hadin gwiwa ta Sin da Afirka ke bunkasa yadda ake bukata. Kamar dai yadda shugaba Bola Tinubu na kasar Najeriya ya fada, a taron kolin dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a bana, cewa ”yayin da ake fuskantar kalubalolin tattalin arziki da na siyasa dake addabar duniya, huldar Afirka da Sin ta nuna yanayi na jajircewa, ta yadda ta zama wani abin koyi ga kasa da kasa.”

 

Dangane da jajircewar da shugaba Tinubu ya ambata, za a samu cikakken bayani ne cikin jawabin da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya yi a jiya Talata, kan ayyukan da aka yi a kasar Sin a fannin diplomasiyya cikin shekarar 2024. A cikin jawabin, Wang ya ambaci sakamakon taron koli na dandalin FOCAC da ya gudana a Beijing a wannan karo, yana cewa, ”Shugabannin Sin da Afirka sun cimma ra’ayi daya, kan gina al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya ta sabon zamani, dake iya jure duk wani yanayi.” To, maganar ”jure duk wani yanayi” da ”jajircewa” suna da ma’ana kusan iri daya. Wato duk wani kalubale da ake fuskanta, kuma duk wata matsalar da ake fama da ita, Sin da Afirka za su yi kokarin neman ci gaba na bai daya, kafada da kafada.

  • Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya
  • Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa

To, sai dai ta yaya ake aiwatar da matsayar da aka cimma? Wang ya ambaci wasu matakan tallafawa kokarin raya kasa guda 8, da Sin take gudanar da su a hadin gwiwarta da dimbin kasashen dake nahiyar Afirka, wadanda suka shafi rage talauci, da samar da isasshen abincin da ake bukata, da kirkiro sabbin fasahohi, da dai sauransu. Kana jami’in ya ambaci yadda kasar Sin ta cire kudin kwastan kan kayayyakin da take shigowa daga kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, da aikin hadin kai da Sin da Afirka ke gudanarwa, mai nasaba da fannoni 10 da suka hada da ciniki da zuba jari, da tsarin samar da kayayyaki, da dai makamantansu.

 

Labarai Masu Nasaba

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

Sai dai don tabbatar da jajircewar huldar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, ban da ingantattun manufofin da ake aiwatar da su a halin yanzu, ana bukatar samun hasashe mai yakini kan makomar huldar. Dangane da wannan fanni, za mu iya duba jawaban da aka yi wajen muhawarar Mjadala Afrika, da ta gudana a kasar Habasha a kwanakin nan. An yi muhawarar ne tsakanin mutane masu takarar neman kujerar shugaban majalissar kungiyar kasashen Afirka ta AU, inda aka ba mutanen da za su iya zama shugaban majalissar kungiyar AU damar bayyana manufofin raya nahiyar Afirka da za su iya dauka a nan gaba, idan sun ci nasarar lashe zaben.

 

Sai dai a bisa ra’ayin ‘yan takara na kasashen Kenya, da Djibouti, da Madagascar, da dai sauransu, makoma mai haske ta nahiyar Afirka ta dogara kan karfafa huldar abota, da za ta tabbatar da kirkire-kirkire, da adalci, da samun ci gaba tare, inda kasar Sin za ta taka rawar gani a ciki.

 

Abun lura shi ne, burikan da wadannan ‘yan siyasa suka ambata a jawabansu, irinsu kokarin gina yankin ciniki cikin ‘yanci na Afirka, da karfafa ciniki tsakanin kasashen Afirka, da amfani da tsarin fasahar dijital wajen sa ido kan yadda ake aiwatar da Ajandar 2063, da inganta kwarewar kasashen Afirka a fannonin tinkarar bazuwar annoba da ke abkuwa ba zato ba tsammani, da nemo kayayyakin aikin jinya da ake bukata, sun dace da matakan hadin gwiwar da ake yi tsakanin Sin da Afirka, da ta shafi aiwatar da shawarar ”Ziri Daya da Hanya Daya”, da yada fasahohin dijital zuwa karin wurare, da aikin jinya, da dai makamantansu. To, wadannan abubuwa sun shaida cewa, akwai tabbaci ga huldar hadin kai ta Sin da Afirka, cikin wani dogon lokaci mai zuwa.

 

Cikin jawabinsa ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kasar Sin za ta yi amfani da yanayin tabbas da take da shi wajen tinkarar yanayin rashin tabbaci da ake fama da shi a duniya. To, a ganina, jajircewar huldar hadin kai tsakani Sin da Afirka ita ma tana samar da tabbaci, da imani, da kwanciyar hankali ga duniyarmu, da ke fama da yanayin tangal-tangal a halin da muke ciki. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya

Next Post

Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

Related

Daurarru
Ra'ayinmu

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

1 week ago
NCC
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

2 months ago
Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
Ra'ayi Riga

Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

2 months ago
Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan
Ra'ayi Riga

Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan

3 months ago
Ra'ayinmu

Gangamin Yaki Da Cutar Kuturta A Nijeriya

3 months ago
Karuwar Cin Zarafi Da Makomar Yara A Nijeriya
Ra'ayinmu

Karuwar Cin Zarafi Da Makomar Yara A Nijeriya

4 months ago
Next Post
Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

LABARAI MASU NASABA

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.