ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Tabbaci Ga Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afirka

Karshen shekara lokaci ne na waiwaye adon tafiya. Sai dai a wannan shekarar da muke ciki, mun gane ma idanunmu dimbin abubuwan takaici da suka abku a duniya. Wani abu da zai iya sanyaya zuciyarmu shi ne, yadda huldar hadin gwiwa ta Sin da Afirka ke bunkasa yadda ake bukata. Kamar dai yadda shugaba Bola Tinubu na kasar Najeriya ya fada, a taron kolin dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a bana, cewa ”yayin da ake fuskantar kalubalolin tattalin arziki da na siyasa dake addabar duniya, huldar Afirka da Sin ta nuna yanayi na jajircewa, ta yadda ta zama wani abin koyi ga kasa da kasa.”

 

Dangane da jajircewar da shugaba Tinubu ya ambata, za a samu cikakken bayani ne cikin jawabin da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya yi a jiya Talata, kan ayyukan da aka yi a kasar Sin a fannin diplomasiyya cikin shekarar 2024. A cikin jawabin, Wang ya ambaci sakamakon taron koli na dandalin FOCAC da ya gudana a Beijing a wannan karo, yana cewa, ”Shugabannin Sin da Afirka sun cimma ra’ayi daya, kan gina al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya ta sabon zamani, dake iya jure duk wani yanayi.” To, maganar ”jure duk wani yanayi” da ”jajircewa” suna da ma’ana kusan iri daya. Wato duk wani kalubale da ake fuskanta, kuma duk wata matsalar da ake fama da ita, Sin da Afirka za su yi kokarin neman ci gaba na bai daya, kafada da kafada.

ADVERTISEMENT
  • Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya
  • Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa

To, sai dai ta yaya ake aiwatar da matsayar da aka cimma? Wang ya ambaci wasu matakan tallafawa kokarin raya kasa guda 8, da Sin take gudanar da su a hadin gwiwarta da dimbin kasashen dake nahiyar Afirka, wadanda suka shafi rage talauci, da samar da isasshen abincin da ake bukata, da kirkiro sabbin fasahohi, da dai sauransu. Kana jami’in ya ambaci yadda kasar Sin ta cire kudin kwastan kan kayayyakin da take shigowa daga kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, da aikin hadin kai da Sin da Afirka ke gudanarwa, mai nasaba da fannoni 10 da suka hada da ciniki da zuba jari, da tsarin samar da kayayyaki, da dai makamantansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

Sai dai don tabbatar da jajircewar huldar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, ban da ingantattun manufofin da ake aiwatar da su a halin yanzu, ana bukatar samun hasashe mai yakini kan makomar huldar. Dangane da wannan fanni, za mu iya duba jawaban da aka yi wajen muhawarar Mjadala Afrika, da ta gudana a kasar Habasha a kwanakin nan. An yi muhawarar ne tsakanin mutane masu takarar neman kujerar shugaban majalissar kungiyar kasashen Afirka ta AU, inda aka ba mutanen da za su iya zama shugaban majalissar kungiyar AU damar bayyana manufofin raya nahiyar Afirka da za su iya dauka a nan gaba, idan sun ci nasarar lashe zaben.

 

Sai dai a bisa ra’ayin ‘yan takara na kasashen Kenya, da Djibouti, da Madagascar, da dai sauransu, makoma mai haske ta nahiyar Afirka ta dogara kan karfafa huldar abota, da za ta tabbatar da kirkire-kirkire, da adalci, da samun ci gaba tare, inda kasar Sin za ta taka rawar gani a ciki.

 

Abun lura shi ne, burikan da wadannan ‘yan siyasa suka ambata a jawabansu, irinsu kokarin gina yankin ciniki cikin ‘yanci na Afirka, da karfafa ciniki tsakanin kasashen Afirka, da amfani da tsarin fasahar dijital wajen sa ido kan yadda ake aiwatar da Ajandar 2063, da inganta kwarewar kasashen Afirka a fannonin tinkarar bazuwar annoba da ke abkuwa ba zato ba tsammani, da nemo kayayyakin aikin jinya da ake bukata, sun dace da matakan hadin gwiwar da ake yi tsakanin Sin da Afirka, da ta shafi aiwatar da shawarar ”Ziri Daya da Hanya Daya”, da yada fasahohin dijital zuwa karin wurare, da aikin jinya, da dai makamantansu. To, wadannan abubuwa sun shaida cewa, akwai tabbaci ga huldar hadin kai ta Sin da Afirka, cikin wani dogon lokaci mai zuwa.

 

Cikin jawabinsa ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kasar Sin za ta yi amfani da yanayin tabbas da take da shi wajen tinkarar yanayin rashin tabbaci da ake fama da shi a duniya. To, a ganina, jajircewar huldar hadin kai tsakani Sin da Afirka ita ma tana samar da tabbaci, da imani, da kwanciyar hankali ga duniyarmu, da ke fama da yanayin tangal-tangal a halin da muke ciki. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Afirka
Ra'ayinmu

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

August 14, 2026
Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG
Ra'ayinmu

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

July 31, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Next Post
Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.