ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Tabbaci Ga Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

Karshen shekara lokaci ne na waiwaye adon tafiya. Sai dai a wannan shekarar da muke ciki, mun gane ma idanunmu dimbin abubuwan takaici da suka abku a duniya. Wani abu da zai iya sanyaya zuciyarmu shi ne, yadda huldar hadin gwiwa ta Sin da Afirka ke bunkasa yadda ake bukata. Kamar dai yadda shugaba Bola Tinubu na kasar Najeriya ya fada, a taron kolin dandalin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da ya gudana a birnin Beijing na kasar Sin a bana, cewa ”yayin da ake fuskantar kalubalolin tattalin arziki da na siyasa dake addabar duniya, huldar Afirka da Sin ta nuna yanayi na jajircewa, ta yadda ta zama wani abin koyi ga kasa da kasa.”

 

Dangane da jajircewar da shugaba Tinubu ya ambata, za a samu cikakken bayani ne cikin jawabin da mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya yi a jiya Talata, kan ayyukan da aka yi a kasar Sin a fannin diplomasiyya cikin shekarar 2024. A cikin jawabin, Wang ya ambaci sakamakon taron koli na dandalin FOCAC da ya gudana a Beijing a wannan karo, yana cewa, ”Shugabannin Sin da Afirka sun cimma ra’ayi daya, kan gina al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya ta sabon zamani, dake iya jure duk wani yanayi.” To, maganar ”jure duk wani yanayi” da ”jajircewa” suna da ma’ana kusan iri daya. Wato duk wani kalubale da ake fuskanta, kuma duk wata matsalar da ake fama da ita, Sin da Afirka za su yi kokarin neman ci gaba na bai daya, kafada da kafada.

ADVERTISEMENT
  • Tattalin Arzikin Kasar Sin A Matsayin Bango Majinginar Duniya
  • Dangote Ya Musanta Labarin Ciyo Bashin NNPC Na Dala Biliyan 1 Domin Tallafa Wa Matatarsa

To, sai dai ta yaya ake aiwatar da matsayar da aka cimma? Wang ya ambaci wasu matakan tallafawa kokarin raya kasa guda 8, da Sin take gudanar da su a hadin gwiwarta da dimbin kasashen dake nahiyar Afirka, wadanda suka shafi rage talauci, da samar da isasshen abincin da ake bukata, da kirkiro sabbin fasahohi, da dai sauransu. Kana jami’in ya ambaci yadda kasar Sin ta cire kudin kwastan kan kayayyakin da take shigowa daga kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba da suka kulla huldar diplomasiyya da ita, da aikin hadin kai da Sin da Afirka ke gudanarwa, mai nasaba da fannoni 10 da suka hada da ciniki da zuba jari, da tsarin samar da kayayyaki, da dai makamantansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Sai dai don tabbatar da jajircewar huldar hadin kai tsakanin Sin da Afirka, ban da ingantattun manufofin da ake aiwatar da su a halin yanzu, ana bukatar samun hasashe mai yakini kan makomar huldar. Dangane da wannan fanni, za mu iya duba jawaban da aka yi wajen muhawarar Mjadala Afrika, da ta gudana a kasar Habasha a kwanakin nan. An yi muhawarar ne tsakanin mutane masu takarar neman kujerar shugaban majalissar kungiyar kasashen Afirka ta AU, inda aka ba mutanen da za su iya zama shugaban majalissar kungiyar AU damar bayyana manufofin raya nahiyar Afirka da za su iya dauka a nan gaba, idan sun ci nasarar lashe zaben.

 

Sai dai a bisa ra’ayin ‘yan takara na kasashen Kenya, da Djibouti, da Madagascar, da dai sauransu, makoma mai haske ta nahiyar Afirka ta dogara kan karfafa huldar abota, da za ta tabbatar da kirkire-kirkire, da adalci, da samun ci gaba tare, inda kasar Sin za ta taka rawar gani a ciki.

 

Abun lura shi ne, burikan da wadannan ‘yan siyasa suka ambata a jawabansu, irinsu kokarin gina yankin ciniki cikin ‘yanci na Afirka, da karfafa ciniki tsakanin kasashen Afirka, da amfani da tsarin fasahar dijital wajen sa ido kan yadda ake aiwatar da Ajandar 2063, da inganta kwarewar kasashen Afirka a fannonin tinkarar bazuwar annoba da ke abkuwa ba zato ba tsammani, da nemo kayayyakin aikin jinya da ake bukata, sun dace da matakan hadin gwiwar da ake yi tsakanin Sin da Afirka, da ta shafi aiwatar da shawarar ”Ziri Daya da Hanya Daya”, da yada fasahohin dijital zuwa karin wurare, da aikin jinya, da dai makamantansu. To, wadannan abubuwa sun shaida cewa, akwai tabbaci ga huldar hadin kai ta Sin da Afirka, cikin wani dogon lokaci mai zuwa.

 

Cikin jawabinsa ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce kasar Sin za ta yi amfani da yanayin tabbas da take da shi wajen tinkarar yanayin rashin tabbaci da ake fama da shi a duniya. To, a ganina, jajircewar huldar hadin kai tsakani Sin da Afirka ita ma tana samar da tabbaci, da imani, da kwanciyar hankali ga duniyarmu, da ke fama da yanayin tangal-tangal a halin da muke ciki. (Bello Wang)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

Xi Ya Bukaci A Zurfafa Ayyukan Farfado Da Yankunan Karkara Da Inganta Karfin Kasar A Fannin Aikin Gona

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.