• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Annobar Cutar Murar Tsuntsaye Ta Yadu A Jihohin Filato Da Katsina

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun bayyana cewa, annobar cutar murar tsintsaye (Bird flu), ta bazu a Jihohin Filato da Katsina.

A makwanni biyu da suka gabata ne, Gwamnatin Tarayya ta ankarar da masu kiwo, musamman na tsintsaye da ofis-ofis na rassan likitocin dabbobi na kasar nan kan barkewar wannan cuta a Jihar Kano.

  • Badakala: Bankin Duniya Ya Kakaba Wa Kamfanoni 2 A Nijeriya Takunkumi
  • NPA Da Kamfanin NLNG Za Su Kulla Hadakar Fitar Da Iskar Gas Ketare

A ranar 23 ga watan Janairun 2025 ne, aka samu rahoton bullar cutar a yankin Farin Gada da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa.

Daraktan duba lafiyar dabbobi na Jihar Filato, Dakta Shase’et Sipak Dawat, a cikin sanarwar da ya fitar a jihar ya bayyana cewa, an samu barkewar annobar murar ce ga kajin gidan gona a wani wajen kiwata su, inda cutar ta harbi tsintsaye sama da 3,000.

Dakta Dawat, ya nuna damuwarsa kan yadda mai kiwon tsintsayen da cutar ta shafa ya sayar da su kafin likitocin dabbobi daga Ma’aikatar Aikin Noma da Raya Karkara su ziyarci wajen kiwon nasa, domin daukar matakan da suka dace.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

“Wannan dalili ne yasa, ake shawartar masu kiwon kajin gidan gonar da su kasance masu sanya idanu tare da tabbatar da tsaftace guraren da suke yin kiwon nasu, domin bai wa tsintsayen da suke kiwatawa kariyar da ta kamata”, in ji Dawat.

Bugu da kari, a Jihar Katsina kuwa, wani jami’in kula da lafiyar dabbobi a shiyyar Karamar Hukumar Malumfashi, Dakta Yau Ishaku; a wani sako da ya isar ga masu kiwon tsintsaye a jihar, ya bayyana bullar annonar a jihar, wanda ya sanar da cewa, ta bulla ne a cikin kwana biyu da suka wuce, kafin samun bullar ta a Jihar Filato.

“Cutar ta bulla ne a Jihar Katsina, a ranar 21 ga watan Janairun 2025, sannan kuma yana da muhimmanci ga daukacin masu kiwon tsitsayen a Kananan Hukumomin Malumfashi, Kafur da Kankara da ke karkashin ofishin shiyya a Karamar Hukumar Malumfashi, da su tabbatar da sun kiyaye wajen daukar matakai, domin kare guraren da suke aiwatar da kiwonsu daga kutsawar wannan annona.”

Ya kara da cewa, ya zama wajibi ga masu kiwon da su rika hana barin mutane suna shiga guraren da suka killace, domin kiwon nasu.

Dakta Yau, ya kuma shawarci masu kiwon da su tabbatar da suna tsaftace kayan da suke amfani da su wajen ciyar da tsitsayen da suke kiwatawa, domin kare su daga kamuwa da cututtuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kashi 85 Na Inibin Da Ake Nomawa Nijeriya, Daga Jihar Kaduna Ne – Dalhatu

Next Post

Abubuwa Biyar Da Ya Kyautu A Mayar Da Hankali A Kansu A Kakar Noman 2025

Related

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 hours ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

4 hours ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

1 week ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

1 week ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

3 weeks ago
Next Post
Aikin Gona

Abubuwa Biyar Da Ya Kyautu A Mayar Da Hankali A Kansu A Kakar Noman 2025

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

July 12, 2025
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.