• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangar Siyasa Ce Silar Rashin Ci Gaban Arewa –Alhaji Ibrahim

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai, Siyasa
0
Bangar Siyasa Ce Silar Rashin Ci Gaban Arewa –Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban gamayyar kungiyoyin matasan arewa mazauna Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci ya nuna takaicinsa da damuwarsa kan yadda arewa ke komawa baya a kowanni bangare, musamman a bangaren ci gaban rayuwa. 

Ya bayyana cewa bangar siyasa ce sillar rashin ci gaban arewa.

  • Za A Sake Yin Gasar Masu Kirkira Da Fasaha Ta Katsina Karo Na Biyu
  • Gwamnatin Kaduna Ta Karyata Jita-jitar Malalar ‘Yan Ta’adda Tsakanin Kaduna Da Zariya

Shugaban ya nuna haka ne a tattaunawarsu da wakilinmu, inda ya ce rashin shugabanni nigari a arewa da a kullum babu abun da suke yi illa tura matasa cikin bangar siyasa.

A cewarsa, “Tabbas matasa na da muhimmancin gaske a kowacce al’umma, tasirinsu ya fi gaban a zura ido kawai ga al’amura ko yanayin yadda suke gudanar da rayuwa.

Wajibi ne da ya hau kan al’umma kan yin tattalin rayuwar matasa, samar da hanyoyin shigar da sakonnin abubuwa masu kyau don su siffantu da su, haka kuma a yi musu bayanin illolin abubuwa marasa kyau don su kaurace musu.”

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Shugaban a ci gaba da bayyana cewa matsalar bangar siyasa ana samu a ko’ina a Nijeriya da ma duniya baki daya, amma na yankin arewa abun ya wuce misali.

Inda ya kara da cewa, “duk wata kasa da ta ci gaba a wannan duniya, idan aka waiwaiyi sirrin da ke tattare da samuwar ci gabanta, za a ga akwai hannun matasansu yake. Saboda ba su yin sakaci a fannin kulawa da rayuwar matasa ba.

“Hakki ne babba wanda ya rataya a wuyan iyaye namu na arewa da su kasance mataki na farko a inda ‘ya ‘yansu za su koyi tarbiyya, mu’amala da mutane, kiyaye dokokin kasa, kauce wa ayyukan barna da dai sauransu.

“Idan matasamu suka hankalta ta hanyar kauracewa bangar siyasa da rikicin zabe, tabbas baragurbin ‘yan siyasa da ba su son zaman lafiya a Nijeriya ba za su kai ga cimma burinsu ba na zubar da jinin mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.

“A matsayinka na matashi, ya kamata ‘yan siyasa su taimake ka wurin gina rayuwarka wajen samar da ayyukan da matasa za su yi na bankwana da zaman banza, a samar masu guraben karatu a makarantun da muke da su.

Wannan shi ne aikin gina rayuwar mutum ba a ba shi makami da kwaya ba. Makami da kwaya sai dai rusa rayuwarka, ya zama ba ka da fata nagari ga kanka da al’ummar da kake tare da su” kamar yadda ya fada.

Daga karshe, ya yi kira ga shugabannin siyasar arewa da su sani sai da zaman lafiya za su iya shugabantar al’umma, idan suka dora matasa a bangar siysa ba za a sami zaman lafiya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SiyasaArewaBangar SiyasaMatasaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

“Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Next Post

Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

6 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

7 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

8 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

9 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

12 hours ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

14 hours ago
Next Post
Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.