Rundunar ‘yansandan Jihar Filato, ta kama wasu mutane hudu da ake zargin ‘yan ƙungiyar asiri ne a ƙauyen Gidan Mai Naraguta, da ke ƙaramar hukumar Jos ta Arewa.
kakakin rundunar, DSP Alfred Alabo, ya ce an samu rahoton cewa waɗannan mutanen na cikin ƙungiyar asiri ta Black Axe wadda ta addabi mutane a yankin.
- Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
- ‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
Bayan samun sahihin bayani, Kwamishinan ‘yansandan jihar ya tura jami’an sashen yaƙi da laifukan yanar gizo da ƙwayoyi zuwa yankin.
An cafke mutane huɗu: Juventus Danladi, Tina Yaro, Douglas Addra, da Yamusa Justine.
Bayan gudanar da bincike a gidajensu, ‘yansanda sun samo bindigogi guda biyu, harsasai, tabar wiwi da sauran kayayyaki.
DSP Alabo, ya ce ana ci gaba da bincike kan lamarin, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.
Kwamishinan ‘yansandan Jihar Filato, CP Emmanuel Olugbemiga Adesina, ya jaddada ƙudirin rundunar wajen yaƙi da laifuka da kuma tabbatar da zaman lafiya a jihar.
Ya kuma roƙi jama’a da su riƙa bai wa ‘yansanda ingantattun bayanai a kan lokaci domin taimaka musu wajen gudanar da aikinsu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp