• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Zan so in koma gida ba tare da bata lokaci ba, don in gabatar da dabarun ga abokanan aikina”. A watan Afrilun bana, tawagar wakilan jam’iyyar UDA mai mulki ta kasar Kenya ta kawo ziyara kasar Sin a karkashin jagorancin babban sakatarenta Mr. Hassan Omar, kuma dabarun jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na gudanar da harkokinta sun burge su matuka. A cewar Mr. Omar, kasar Sin tana da kwarewa da dabarun saukaka fatara da tabbatar da adalci ga al’umma, wadanda suke iya zama abin koyi ga Kenya a kokarinta na aiwatar da gyare-gyare ga tattalin arziki da zaman al’umma da kuma siyasa. 

A ganin mambobin tawagar Kenya, idan ana son fahimtar dalilin ci gaban kasar Sin, dole ne a fara da fahimtar jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tukuna, kuma wannan ra’ayi yana ta kara samun karbuwa a tsakanin karin ‘yan siyasa da kwararrun masana na kasashe daban daban. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin jam’iyya ce mai mulki a kasar, wadda aka kafa ta a shekarar 1921, kuma kawo yanzu shekarunta sun kai 104. Me ya sa jam’iyyar mai tsawon tarihi na sama da shekaru 100 har yanzu take dorewa a kan mulki? A ganina, babban dalili shi ne yadda jam’iyyar take daukar jama’a a matsayin tushen ayyukan da take sanyawa a gaba. A shekaru 80 da suka wuce, an taba yi wa tsohon jagoran jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin marigayi Mao Zedong tambaya cewa, ta yaya jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin zata iya dorewa? Ya amsa da cewa, “A bar jama’a su sa ido a kan aikin gwamnati”. Sai kuma da muka shiga sabon zamani, jam’iyyar ta gano sabuwar mafita, wato a dinga yi wa jam’iyyar kwaskwarima. Kamar yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ce, “Kasa ita ce jama’a, kuma jama’a su ne kasa. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta jagoranci jama’a su kafa kasarsu da kiyaye ta, domin kiyaye imanin jama’a a kan ta.” Lallai bauta wa jama’a bisa iya kokarinta, shi yake samar wa jam’iyyar kwarin gwiwa da niyyar yi wa kanta kwaskwarima, haka kuma shi ne ainihin dalilin da ya sa take samun goyon baya daga jama’a.

  • David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
  • Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

“Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana samun farin jini wurin jama’a, wannan kuma shi ne sirrin nasarorin da ta samu. Manufar gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya da ta gabatar ma tana shafar jama’a. Aminaina Sinawa su kan ce ‘kada mu manta da ainihin abin da muke neman cimmawa’, to, a ganina wannan shi ne abin da ake neman cimmawa”, in ji Jose Julio Gomez Beato, jakadan kasar Dominica a kasar Sin. Abin hakan yake, tun farkon kafuwarta, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta mai da samar wa al’umma alheri da kuma farfado da al’ummar Sinawa a matsayin ainihin abin da take neman cimmawa. Sai dai ba kamar jam’iyyun siyasa na wasu kasashe da su kan jaddada sanya kasashensu a gaba da kome ba, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin a nata bangare tana kokarin amfanar al’ummar kasar, tana kuma kokartawa don tabbatar da ganin ci gaban dan Adam baki daya, wannan kuma shi ne dalilin da ya sa ta gabatar da manufarta ta “gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya”.

Alkaluman da aka samar a ranar 30 ga watan Yunin da ya gabata sun nuna cewa, kawo karshen bara, yawan ‘yan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya zarce miliyan 100, kuma yawan wadanda suka mika rokonsu na zama ‘ya‘yan jam’iyyar ya wuce miliyan 20, alkaluman da kuma suka shaida jam’iyyar na matukar samun karbuwa a tsakanin al’ummar kasar.

Tun bayan kafuwarta shekaru 104 da suka gabata, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta jagoranci jama’ar kasar wajen samun nasarar juyin juya hali a kasar, daga nan kuma, ta jagoranci jama’ar kasar wajen tabbatar da saurin bunkasar tattalin arziki da al’umma mai zaman lumana a kasar, nasarorin da suka kasance na a zo a gani a duniya. Sabo da jama’a take kokartawa, kuma ta dogara da jama’a wajen cimma nasara.

Labarai Masu Nasaba

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

‘Yan tawagar jam’iyyar UDA ta kasar Kenya da suka kawo ziyara kasar Sin sun kwatanta jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin da bishiyar kuka, suna cewa, “Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tamkar bishiyar kuka ce, wadda ke da ingantattun saiwoyi da ma babban karfi na warkar da kanta, tana ta fid da furanni da ‘ya’ya ba tare da tsayawa ba” “bishiyoyin kuka suna da tsawon rai na sama da shekaru dubu”. Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin tana cikin karfinta, kuma za ta ci gaba da kokartawa domin bauta wa jama’a, tare da dogara da jama’a don cimma karin nasarori.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka

Next Post

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Related

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

4 days ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

4 days ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

1 week ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

1 week ago
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”
Ra'ayi Riga

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

1 week ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Jks

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.