• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

by Leadership Hausa
4 weeks ago
in Manyan Labarai
0
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zanga-zangar da ‘yan gudun hijira biyo bayan hare-haren da ya tarwatsasu daga matsugnanunsu da ke a yankin Yelwata, na jihar Biniwe, hakan ya nuna a zahiri, na irin yanayin yin watsi da ‘yan gudun hijira a kasar.

Sun yi zanga-zngar ce, a wasu manyan titnun kamar na George Akume da ke a Makurdi, babban birinin jihar, a ranar 19 na watan Yunin, 2025.

  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Sun datse hanyoyin, domin su nuna bacin ransu, na barinsu na yin watsi da su a sansaninsu da barinsu a cikin yanwa da kuma karkatar da kayan da aka turo masu na dauki.

Abin takaici ne, duba da yadda ake samun sansanin ‘yan gudun hijira a kasar makare da masu gudun hijira, ba tare da an tanadar masu da kayan more rayuwa ba, wanda rashin hakan, ke janyo mutuwar wasunsu.

Tabbas, irin wannan halin da suke ciki, abu ne, da ke bukatar a dauki matakan gaggawa, domin magance wadannan matsalolin.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

Kazalika, gazawar Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA da kuma sauran hukumomin na jihohi na sauke nauyinsu, hakan ya nuna a zahiri, na irin kalubalen da ake fuskanta, na rashin sauke nauyinsu, na bayar da agajin na gaggawa.

Misalii, an ruwaito cewa, a sansanin na ‘yan gudun hijira na Yelwata, musamman yadda suke kwana a kan tandarmin kasa, tare da kokawa da cizon Sauro, ‘ya’yansu ke ci gaba da zama a cikin yunwa, wanda hakan, ya kara harzuka su, fita yin zanga-zangar.

Bisa wasu akaluma da aka samu daga Biniwe, sun nuna cewa, a sansanin na Yelwata, an samu haihuwa 15 da kuma mata da suka samu juna biyu, su 122, wadanda kuma suke ci gaba da rashin samun kulawar kiwon lafiyarsu, hakan kuma ya jefa, rayuwar jariransu, a cikin hadari.

Bugu da kari, a sansanin ‘yan gudun hijira na jihar Nasarawa, an samu kwararowar sama da ‘yan gudun hijira guda 4,000 daga sansanin ‘yan gudun hijira na Biniwe.

Wannan ya zama wani babban nauyin wajen ciyar da su da kuma rashin samar masu da wajen wadatattun wajen kwana da rashin tsafta.

Kusan a daukacin sansanonin ‘yan gudun hijira, kamar na jihohin Borno da Adamawa, dubban ‘yan gudun hijirar da yaki da ‘yan ta’addar Boko Haram ya tarwatsa su daga matsugunan su, suna ci gaba da fuskantar karancin ruwan sha, magunguna, inda kuma ake samun barkewar Kwalara, wanda hakan, ke janyo rasa rayukan wadanda lamarin ya rutsa da su.

Wadannan misalan kadai, sun nuna irin rashin gazawar kula da yanayin da bil’Adama ke ciki.

Hukumar NEMA, wadda aka dora mata nauyin bayar da dauki kan aukuwar annoba, ta gaza sauke wannan nayin nata.

Sai dai, har yanzu zamu ci gaba da yin magana domin NEMA ta sauke nauyin da aka dora mata, musamman na bayar da agajin na gaggawa ga wadanda wani iftila’i, ya fada masu.

Kazalika, kayan agajin da Hukumar ta tura zuwa sansani na Yelwata, bayan kai hare-haren a yankin, idan aka yi dubi da lokacin da aka kai kayan da rashin kai wadatattunsu, wannan babban abin tambaya ne da har yanzu, ke bukatar amsa, musamman, kan yadda aka zargin wasu jami’an na NEMA, na karkatar da kayan na agajin.

Bugu da kari, hakan ya nuna irin yadda a 2024, NEMA ta fuskanci suka da zargi, na boye kayan da ya kamata a rabawa ‘yan gudun hijira a dakunanta na adana kayan agaji, wanda hakan ya jefa rayuwar ‘yan gudun hijira, musamman wadanda ke a Arewa Masu Gabas, a cikin kuncin rayuwa.

A dai jihar ta Biniwe, Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa ta jihar SEMA, ta fuskanci suka kan yin watsi da ‘yan gudun hijira na Yelwata, musamman duba da yadda aka barsu, a cikin kangin yunwa, cizon Sauro, wanda kuma aka yi zargin, wasu jami’an na SEMA, sun karkatar da kayan agajin, da ya kamata a raba masu.

Hakan ma batun ma yake a jihar Adamawa, inda aka zargi Hukumar SEMA ta jihar, kan kin rabar masu da kayan dauki kan lokaci, wanda hakan ya haifar da zanga-zanga a watan Mayun 2025.

Sai dai, wadanan Hukumomin suna bugewa da dora laifin kan rashin ba su kudaden da ya kamata Gwamnatin Tarayya ta tura masu.

Hakazalika, rashin taka rawar da ya kamata ‘yan majalisu da matakan gwamnati ya kamata su yi, na rabar da kayan dauki ga alumma, hakan ya kara kawo rudani, kan batun na bayar da daukin.

Shirye-shiryen rabar da kayan tallafin rage radadin kuncin rayuwa, hakan ya sanya an fifita mazauna birane da ‘yan lelen ‘yan siyasa, inda su kuma ‘yan gudun hijira, aka mayar da su, saniyar ware.

A jihar ta Biniwe duk da kudaden da gwamnatin jihar kebewa da kananan hukumomin jihar da kuma wanda take kebewa sarakunan gargajiya, amma abin bakin cikin shi ne, ba kebe kudaden, da ya kamata a tallafawa ‘yan gudun hijira na jihar, inda gwamnatin ke fakewa, da cewa, tana fuskantar karancin kudade.

Karkatar da kayan agajin da ya kamata a kai wa ‘yan gudun hijirar na Yelwata, hakan ya nuna cewa, ba a dauki rayuwarsu, da wata mahimmanci ba.

Bisa ra’ayin wannan Jaridar, ya zama wajibi zababbun ‘yan majalisar kasar, su mayar da hankali wajen fifita kula da rayuwar ‘yan gudun hijira, musamman ta hanyar kebe masu wani gwa-gwaban kaso a cikin kasafin kudi na kasar da kuma kirkiro da dokokin da za su tabbatar da an yi adalci, wajen rabar masu da kayan tallafi da kuma daukar kwakwaran hukunci, ga duk wanda ya karkatar da kayan tallafin da aka yi niyyar kai masu.

Bugu da kari, ya zama wajbi matakan gwamnati uku na kasar da su kebe kudade da za a rinka taimaka wa ‘yan gudun hijira kai tsaye da ke a sansanonin su da samar masu da abinci, da kayan kula da lafiyarsu da wajen kwana da kuma sanya ido kan kayan domin a dakile yin cuwa-cuwa da kayan.

Ya zama wajbi kananan hukumomi da masarautu da gwamnatin jihohi ke tallafa masu da kudaden gudanar da ayyukansu, su yi hadaka da jagororin alummomi domin su gano tare da ganin ana tallafa wa ‘yan gudun hijirar, yadda ya dace.

Hakazalika, ya zama wajibi, a yiwa hukumomin NEMA da SEMA garanbawul, musamman domin a dawo da ainahin kimarsu, yadda ya kamata.

Zanga-zangar ta ‘yan gudun hijirar na Yelwata, wata ‘yar manuniya ce, da ke nuni da cewa, ya zama wajbi, a dauki matakan da suka wajaba, na irin halin da suke ciki.

Duba da cewa, a Nijeriya akwai ‘yan gudun hijira da yawansu ya kai sama da miliyan uku, hakan ya nuna cewa, ba wai kawai alkarin baki ya suka cancanta ba, amma kula da rayuwarsu, yadda ta kama, shi ne mafita.

Kazalika, duba da cewa, ana cikin yanayi na damina a kasar, akwai kuma wani karin barazanar da ke tafe, mai yuwa za a iya samun ambaliyar rayuwan sama wanda hakan zai janyo tarwatsa alumomi daga matsugunasu, inda hakan ya nuna cewa, tun yanzu, ya zama waji, a dauki matakan gaggawa.

Ya kamata ‘yan majalisa da shugabannin kananan hukomin da sarakunan gargajiya, su nuna cewa, da gaske suke wajen jin kan rayuwar ‘yan gudun hijira, sama da na su kudurorin na kashin kansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: YelewataZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

Next Post

Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

Related

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

8 hours ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

10 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

12 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

14 hours ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

17 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

1 day ago
Next Post
Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

Ayyukan 'Yan Ta'adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.