• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

by Leadership Hausa
9 hours ago
in Manyan Labarai
0
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsarin Nijeriya ya nuna cewa, kasa ce, mai ala’adu iri da ban da ban wadda kuma take dauke da wasu jama’a da ke aikata, manyan laifuka.

A bisa irin wannan yanayin ne, akawai bukatar a hada kai tare a yi aiki tare da hukumomin tsaro na kasar.

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

Duba da cewa, hukumomin tsaro a kasar na ci gaba da rike ayyukansu na sirrin tsaro, musamman saboda gasar da suke yi da sauran hukumomin tsaro na kasar domin kar su shiga bansu, wajen gudanr da ayyukansu, na samar da tsaro.

Sai dai, ya zama wajbi, a kawo karshen irin wannan gasar da ke a tsakanin hukumomin tsaron, matukar dai, ana bukatar a kawo karshen kalubalen rashin tsaro da ke ci gaba da addamar Nijeriya.

Bisa dokar Nijeriya Cap 278 ta shekarar 1986, kasar ta kasance ta na da hukumomin tsaro na sirri guda uku ne, bayan rusa rundunar hukumar tsaro ta kasa wato NSO.

Labarai Masu Nasaba

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Hukumomin tsaron uku su ne, na DIA, DSS da kuma NIA, inda kuma dokar, ta bayar da damar kafa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a fannin tsaro wato ONSA, wadda a baya, ake kiran ofishin da Babban Jami’in Tsaro na Kasa wato CONS.

Wannan Jaridar, na nuna matukar damauwarta kan ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro, da Nijeriya ke fuskata, musamman na rashin gazawar hukumomin tsaro na sirri saboda gasar da suke nuna wa, a tsakaninsu.

A bisa ra’ayinmu, wannan matsalar, abu ne da ke bukatar a kara mayar da hankali cikin gaggawa domin a magance wannan kalubalen na rashin na rashin tsaron.

Sai dai, muna kuma yabawa kokarin da hukumomin tsaron ke ci gaba da yi, na lalubo da mafita kan kalubalen na rashin tsaro.

Amma abin takaici ne, kan yadda gasar a tsakanin hukumomin tsaron kasar, ke kara haifar da kalubalen na rashin tsaro wanda kamata ya yi ace, suna yin aiki tare, domin a samar wa da ‘yan Nijeriya sauki, wajen magance masu kalubalen rashin tsaron, da suke ci gaba da fuskanta.

Hatta shi ma tsohon Babban Hafsan Tasron kasar ya tabbatar da cewa, akwai bukatar hukumomin tsaro na sirri na kasar, su kara zagaewa wajen samar da dabarun kara ciyar da hukumomin na tsaro.

Wasu kwararru na ganin cewa, akwai bukatar hukumomin tsaron su hada kai domin samar da tsaro a kasar.

Gasar da ke ci gaba da aukuwa a tsakanin hukomomin tsaron su kasance suna samar da bayanan sirri a tsakaninsu, domin a dakile kalubalen rashin tsaro a kasar.

Masu ruwa da tsaki a kasar, ciki har da shugaba Bola Ahmed Tinubu, na ci gaba da nuna damuwarsu, kan kalubalen rashin tsaro a kasar, musamman duba da yadda Tinubu, a wani taro na kwanan baya ya sanar da cewa, kalubalen rashin tsaro a karni na 21, abu ne da ake bukatar hada kai, amma ba wai batun nuna yin gasa, a tsakanin hukumomin tsaron kasar ba.

Kalubalen ta’addanci a Arewa Maso Gabas, matsalar ayyukan ‘yan bindiga a Arewa Maso Yamma, fashi a Tekunan ruwa a Tekun Guinea, rikicin manoma da makiyaya a yankin Middle-Belt, batun ‘yan aware a yankin Kudu Maso Gabas, wadannan matsalolin, abu ne, da yafi karfin hukumar tsaro daya, ta kawo karshensu.

Kazalika, hare-haren da suka janoyo kashe wasu kauyawa kimanin su 200 a daren ranar 13 na watan Yunin 2025 yankin Yelwata, na karamar hukumar Guma a jihar Biniwe da kuma sake dawor ayyukan ‘yan ta’addar Boko Haram a yankin Arewa Maso Gabas, hakan ya nuna a zahiri, akwai bukatar hukumomin tsaron su hada kai domin tunkarar kalubalen na rashin tsaro da kuma kawo karshen sa, musamman duba da cewa, matsalar na kara zama barazana ga tattalin arzikin.

Sai dai, hakan ya nuna cewa, kusan babu wani katabus da hukumomin tsaron ke yi, na magance kalubalen na rashin tsaron.

A ra’ayin wannan Jaridar, akwai matukar bukatar Gwamnati ta dauki kwararan matakai, musamman domin gano ainahin tushen matsalar ta rashin tsaro, da kuma magance ta.

Sai dai, wani kokari daya shi ne, na kara fadada mahukuntan na tsaron sirri wato kafa cibiyar kasa ta dakile yunkurin ayyukan ta’addanci NCTC.

Bukatar hukumomin tsaron na sirri, na yin aiki a tare, abu ne da yake da matukar mahimmanci, musamman domin a magance kalubalen rashin tsaro, da Nijeriya ke fusanta.

Ra’ayin wannan Jaridar shi ne, akwai bukatar hukumomin tsaro na sirri na kasar, su jingine batun gasa a tsakaninsu, su mayar da hankali, wajen lalubo da mafita, kan kalubalen rashin tsaro a kasar.

Kazalika, duba da irin yanayin na barazar rashin tsaron, ya kamata a kara zuba kudade wajen kara darajar kayan kimiyya na aikin tsaro na hukumomin tsaron kasar, wanda hakan zai kara masu kwarin guiwar, kara mayar da hankali a ayyukansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jami'an TsaroNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Next Post

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Related

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

2 hours ago
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote
Manyan Labarai

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

4 hours ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

4 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

8 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

19 hours ago
Next Post
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

LABARAI MASU NASABA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

July 11, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

July 11, 2025
Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga

Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga

July 11, 2025
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara

July 11, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

July 11, 2025
Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

July 11, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.