• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’ummar da ke yankin Mumuye a jihar Taraba, akasarinsu manoman doya ne kuma ta nan ne suke samun kudin biyan bukatunsu na yau da kullum.

A karamar hukumar Yorro da Zing an san al’ummar Mumuye wajen noman doya saboda haka suka kasance a kan gaba wajen noman doya a jihar.

  • Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

Sai dai, babban kalubalen da suke fama da shi, shi ne na rashin hanya mai kyau da za su dinga yin safarar doyar da suka noma zuwa kasuwani, musamman kasuwannin da ke makwabtaka da jihar, inda ‘yan na-kama ke yin amfani da wannan damar wajen sayen doyar da suka hake da araha.

A dukkan kananan hukumomin biyu, babu wata shinfidaddiyar kwalata da gwamnatin jihar ta yi, musamman babbar hanyar da za ta sada sauran kauyukan da ke a yankunan.
Hanya daya da ta hada shalkwatar Pantisawa da ke a karamar hukumar Yorro da babbar hanyar Jalingo zuwa Yola, gwamnatin jihar Filato ce ta bayar da kwangilar ta, har yanzu ba a kammala ta ba.

Har ila yau, aikin babbar hanya daga Zing zuwa Monkin wanda aikin mazaba ne da mariganyiya Sanata Jummai Ai’sha Alhassan ta faro shi, sima an yi wasti da aikin.

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Wata mace mai noman doya a yankin Nyadadi Gorko da ke a Yorro Zulai Muhammed ta koka ne a kan rashin hanya a daukacin yankin na Mumuye, inda ta kara da cewa, ba wani talafa da suke samu daga gun gwamnati kamar yadda gwamnatin ta ke yi wa manoman shinkafa da masara da kuma sauran manoman da ke noma sauran amfanain gona.

Zulai ta ci gaba da cerwa, noman doya abu ne mai wuyar gaske, domin aiki ne da ake shafe wata goma sha biyu ana gudanar da shi, da ya hada da, gyran gona, yin shuka da kuma yin girbi.

A cewarta, akasari ana fara gyaran gona ne a cikin watan Satumba, inda kuma ake fara yin shuka daga a watan Disamba, sannan kuma a hake ta a cikin watan Satumba, inda hakan ke nuna cewa, ana shafe shekara daya ne ana yin aikinta.

Zulai ta ce, manomamn doya na yin amfani da takin zamani kala biyu ne da wanda ke sa doyar saurin girma wato NPK da kuma wanda ke sa jijiyar doyar yin girma, inda ta kara da cewa, irin na doya da ake shuka wa yana tsada, inda hakan ke sanya wa sabon shiga cikin fannin bas a samu wata riba kirki.

Shi ma wani manomin na doya a yankin Haruna Hassan ya sanar da cewa, rashin yin kulawar da ta dace a fannin na jawo wa manomanta rashin samun riba mai yawa, wanda ya ce, akasarin manoman doya a yankunan har yanzu suna yin noman na ta hanyar gargakiya ganin cewa, ba a tanadar masu da kayan aiki na zamani ba.

Bugu da kari shi ma wani manomin doya a karamar hukumar Zing Bulus Shamaki ya bayyana cewa, akasarin maomnaon da ke Mumuye na sayar da wani kashi na doyar da suka noma ne domin su samarwa da kansu kuadaden shiga.

Ya sanar da cewa, akwai bukatar manoman na doya, musamman a yankuna da su hada kansu waje daya su kafa kungiya don yin magana da yawu daya a kan matsalolinsu da kuma yadda za su dinga samun rance don kara fadada sana’ar ta su.

Bugu da kari, shi ma wani manomin doya mai suna Yarima Isa Tafida anda ke da gona a Mumuye ya sanar da cewa, ya na nomanta da yawa.

A bisa wani bincike da aka gudanar ya nuna cewa, ana sayar manyan kwaryar doya a kan farashin naira 150,000, inda kuma ake sayar da kanana daga naira 45,000 zuwa naira 100,000.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Taya Murnar Kafuwar Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Bunkasa Kirkire-Kirkire Da Ilimi Domin Wanzar Da Ci Gaba A Fannin Sufuri

Next Post

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

3 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

3 days ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.