• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Wasu Manoma Kan Fuskanci Matsalar Sarrafa Amfanin Gona

by Abubakar Abba
3 years ago
Manoma

A Nijeriya baya ga noman damina da manoman kasar ke yi, akwai kuma manoman da ke yin noman rani bayan daminar ta wuce, inda hakan ke kara taimaka musu wajen kara samar wa da kansu kudi da kuma kara wadata kasar da abinci.

Wasu masana na ganin cewa kokarin nasu bai kai ga yadda za a iya yayata wa ba, domin kuwa a ganinsu da a ce ana aiwatar da abubuwan da ake fada a baki, da yanzu kasar ta dara takwarorinta da suka yi mata nisa wajen noman rani.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni

A cewar masanan, Nijeriya za ta iya shiga gaban kasar Masar, wajen noman tumatir, saboda idan ka duba, kashi saba’in cikin dari na kasar Masar sahara ce, inda kuma Nijeriya, Allah ya albarkace ta da kasar noma mai inganci, amma ba ma bin hanyoyin da suka dace.

Masana dai na da ra’ayin cewa, hukumomi a Nijeriya har yanzu ba sa fargabar ganin yadda suke yi wa sashin na noma rikon Sakanaira Kashi.
Duk da cewa kasar na daga manyan masu noman tumatur a duniya, har yanzu kasar na shigo da tumatur daga kasashen waje.

Alhaji Abdulrahim Ali, wani manomi a karamar hukumar Kura ta jihar Kano, ya sanar da cewa, suna noman tumatir, amma idan masu siya ba su zoba ba, dole ne mu dauka mu kai kasuwa mu siyar da araha.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Shi kuwa Malam Danlami Umar, sakatare na Kungiyar masu sai da kayan gwari ta jihar Kano, ya bayyana cewa, wannan shi ne lokacin da ake asara, saboda tsananin tsadar da kayan ke da shi.

Ya kara da cewa, idan ka je gonar wani manomin za ka samu kaya mai yawa.

Kokarin Gwamnati
Kwamishinan noma na jihar Kano Alhaji Musa Sulaiman Shanono ya ce, gwamnatin tana kokarinta wajen magance wanan matsala.

Alhaji Musa ya kara da cewa, gwamnati tana sane kuma ta damu kwarai, saboda haka gwamnatin kano ta kulla yarjejeniya domin samar da kamfanin da zai dinga sarrafa tumatir domin taimaka wa manoma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Kyautata Dokoki Domin Samun Ci Gaba Mai Dorewa A Bangaren Teku

Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Kyautata Dokoki Domin Samun Ci Gaba Mai Dorewa A Bangaren Teku

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.