• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Wasu Manoma Kan Fuskanci Matsalar Sarrafa Amfanin Gona

by Abubakar Abba
3 years ago
Manoma

A Nijeriya baya ga noman damina da manoman kasar ke yi, akwai kuma manoman da ke yin noman rani bayan daminar ta wuce, inda hakan ke kara taimaka musu wajen kara samar wa da kansu kudi da kuma kara wadata kasar da abinci.

Wasu masana na ganin cewa kokarin nasu bai kai ga yadda za a iya yayata wa ba, domin kuwa a ganinsu da a ce ana aiwatar da abubuwan da ake fada a baki, da yanzu kasar ta dara takwarorinta da suka yi mata nisa wajen noman rani.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni

A cewar masanan, Nijeriya za ta iya shiga gaban kasar Masar, wajen noman tumatir, saboda idan ka duba, kashi saba’in cikin dari na kasar Masar sahara ce, inda kuma Nijeriya, Allah ya albarkace ta da kasar noma mai inganci, amma ba ma bin hanyoyin da suka dace.

Masana dai na da ra’ayin cewa, hukumomi a Nijeriya har yanzu ba sa fargabar ganin yadda suke yi wa sashin na noma rikon Sakanaira Kashi.
Duk da cewa kasar na daga manyan masu noman tumatur a duniya, har yanzu kasar na shigo da tumatur daga kasashen waje.

Alhaji Abdulrahim Ali, wani manomi a karamar hukumar Kura ta jihar Kano, ya sanar da cewa, suna noman tumatir, amma idan masu siya ba su zoba ba, dole ne mu dauka mu kai kasuwa mu siyar da araha.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Shi kuwa Malam Danlami Umar, sakatare na Kungiyar masu sai da kayan gwari ta jihar Kano, ya bayyana cewa, wannan shi ne lokacin da ake asara, saboda tsananin tsadar da kayan ke da shi.

Ya kara da cewa, idan ka je gonar wani manomin za ka samu kaya mai yawa.

Kokarin Gwamnati
Kwamishinan noma na jihar Kano Alhaji Musa Sulaiman Shanono ya ce, gwamnatin tana kokarinta wajen magance wanan matsala.

Alhaji Musa ya kara da cewa, gwamnati tana sane kuma ta damu kwarai, saboda haka gwamnatin kano ta kulla yarjejeniya domin samar da kamfanin da zai dinga sarrafa tumatir domin taimaka wa manoma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
Noma Da Kiwo

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Noma Da Kiwo

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Kyautata Dokoki Domin Samun Ci Gaba Mai Dorewa A Bangaren Teku

Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Kyautata Dokoki Domin Samun Ci Gaba Mai Dorewa A Bangaren Teku

LABARAI MASU NASABA

Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025
Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

October 12, 2025
Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.