• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyu Masu Hatsari Da Peter Obi Ya Haddasa A Siyasar Nijeriya –Fadar Shugaban Kasa

•Ku Nemo Hanyar Warware Bashin Da Kuke Lafta Wa Nijeriya - Obi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
peter

Fadar shugaban kasa ta zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi bisa shigo da wasu abubuwa guda biyu masu hatsari a cikin siyasar Nijeriya a zaben da ya gabata.

Mashawarcin shugaban kasa, Bayo Onanuga, shi ne ya zargi Peter Obi da shigo da addini da kabilanci cikin siyasar Nijeriya a lokacin zaben 2023.

  • Mun Dukufa Magance Matsalolin Bangaren Lantarki, In Ji Minista
  • Yadda Musulmi Ke Shirye-shiryen Bikin Karamar Sallah Cikin Tsadar Rayuwa

Mashawarcin shugaban kasan ya bayyana hakan ne a wani shirin gidan rediyo tare da Seun Okinbaloye, inda ya tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta mayar da hankali kan abubuwan da ta sa a gaba na ci gaba ba damuwa da maganganun ‘yan adawa ba.

Onanuga Ya bayyana hakan ne domin mayar da martini ga Peter Obi bisa kalaman da ya yi cewa ya damu kwarai da yadda gwamnatin APC take ci gaba da kinkimo bashi a gida waje.

A dai cikin wannan makon ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ya nuna damuwarsa kan yadda gwamnatin APC ke ci gaba da ciyo wa ‘yan Nijeriya bashi a shafinsa na twitter. “A sulusin farko na 2023, ana bin Nijeriya bashin naira tiriliyan 87.9, inda aka samu karin naira tiriliyan 10 a karshen shekarar 2023. Wannan babban abun takaici ne kuma ya kamata gwamnatin APC ta nemo hanyar warware lamura ba ta hanyar bashi ba,” in ji Obi.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

A martanin nasa, Onanuga ya ci gaba da cewa gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ba ta damuwa ko mayar da hankali kan Peter Obi da magoya bayansa.

Mashawarcin ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da yin aiki tukuru ba tare da damuwa da zargin ‘yan adawa ba.

“A yanzu haka, mun mayar da hankali kan gudanar da harkokin gwamnati kuma ba mu son a karkatar da hankalinmu kan abin da gwamnati ta saka gaba a kai. A kowani lokaci muna cikin aiki ba mu ko kallon ‘yan adawa masu suka.

“Abin da na sani game da yakin neman zaben Peter Obi shi ne, a karon farko a tarihin siyasar Nijeriya mun sami dan takara da ya bijiro da tsattsauran ra’ayin kabilanci da addini wanda ya yi amfani da su domin cin zabe. Wadannan abubuwa guda biyu suna da matukar hatsari a cikin siyasar Nijeriya.

“Lallai wadannan abubuwa guda biyu suna da matukar tsari ga siyasar Nijeriya a halin yanzu,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
PDP

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

LABARAI MASU NASABA

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.