• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyu Masu Hatsari Da Peter Obi Ya Haddasa A Siyasar Nijeriya –Fadar Shugaban Kasa

•Ku Nemo Hanyar Warware Bashin Da Kuke Lafta Wa Nijeriya - Obi

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
peter
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fadar shugaban kasa ta zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi bisa shigo da wasu abubuwa guda biyu masu hatsari a cikin siyasar Nijeriya a zaben da ya gabata.

Mashawarcin shugaban kasa, Bayo Onanuga, shi ne ya zargi Peter Obi da shigo da addini da kabilanci cikin siyasar Nijeriya a lokacin zaben 2023.

  • Mun Dukufa Magance Matsalolin Bangaren Lantarki, In Ji Minista
  • Yadda Musulmi Ke Shirye-shiryen Bikin Karamar Sallah Cikin Tsadar Rayuwa

Mashawarcin shugaban kasan ya bayyana hakan ne a wani shirin gidan rediyo tare da Seun Okinbaloye, inda ya tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta mayar da hankali kan abubuwan da ta sa a gaba na ci gaba ba damuwa da maganganun ‘yan adawa ba.

Onanuga Ya bayyana hakan ne domin mayar da martini ga Peter Obi bisa kalaman da ya yi cewa ya damu kwarai da yadda gwamnatin APC take ci gaba da kinkimo bashi a gida waje.

A dai cikin wannan makon ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ya nuna damuwarsa kan yadda gwamnatin APC ke ci gaba da ciyo wa ‘yan Nijeriya bashi a shafinsa na twitter. “A sulusin farko na 2023, ana bin Nijeriya bashin naira tiriliyan 87.9, inda aka samu karin naira tiriliyan 10 a karshen shekarar 2023. Wannan babban abun takaici ne kuma ya kamata gwamnatin APC ta nemo hanyar warware lamura ba ta hanyar bashi ba,” in ji Obi.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

A martanin nasa, Onanuga ya ci gaba da cewa gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ba ta damuwa ko mayar da hankali kan Peter Obi da magoya bayansa.

Mashawarcin ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da yin aiki tukuru ba tare da damuwa da zargin ‘yan adawa ba.

“A yanzu haka, mun mayar da hankali kan gudanar da harkokin gwamnati kuma ba mu son a karkatar da hankalinmu kan abin da gwamnati ta saka gaba a kai. A kowani lokaci muna cikin aiki ba mu ko kallon ‘yan adawa masu suka.

“Abin da na sani game da yakin neman zaben Peter Obi shi ne, a karon farko a tarihin siyasar Nijeriya mun sami dan takara da ya bijiro da tsattsauran ra’ayin kabilanci da addini wanda ya yi amfani da su domin cin zabe. Wadannan abubuwa guda biyu suna da matukar hatsari a cikin siyasar Nijeriya.

“Lallai wadannan abubuwa guda biyu suna da matukar tsari ga siyasar Nijeriya a halin yanzu,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Baya Ta Haihu: INEC Ta Rushe Babban Taron Jam’iyyar LP Na Kasa

Next Post

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
PDP

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

LABARAI MASU NASABA

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

Gwamnatin Kano Za Ta Mayar Da Gidan Gyaran Hali Na Kurmawa Gidan Tarihi

August 4, 2025
Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

Kashe N712bn Kan Gyaran Filin Jiragen Saman Legas Rashin Sanin Ya Kamata Ne – ADC 

August 4, 2025
Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.