• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyu Masu Hatsari Da Peter Obi Ya Haddasa A Siyasar Nijeriya –Fadar Shugaban Kasa

•Ku Nemo Hanyar Warware Bashin Da Kuke Lafta Wa Nijeriya - Obi

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
peter
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fadar shugaban kasa ta zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi bisa shigo da wasu abubuwa guda biyu masu hatsari a cikin siyasar Nijeriya a zaben da ya gabata.

Mashawarcin shugaban kasa, Bayo Onanuga, shi ne ya zargi Peter Obi da shigo da addini da kabilanci cikin siyasar Nijeriya a lokacin zaben 2023.

  • Mun Dukufa Magance Matsalolin Bangaren Lantarki, In Ji Minista
  • Yadda Musulmi Ke Shirye-shiryen Bikin Karamar Sallah Cikin Tsadar Rayuwa

Mashawarcin shugaban kasan ya bayyana hakan ne a wani shirin gidan rediyo tare da Seun Okinbaloye, inda ya tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta mayar da hankali kan abubuwan da ta sa a gaba na ci gaba ba damuwa da maganganun ‘yan adawa ba.

Onanuga Ya bayyana hakan ne domin mayar da martini ga Peter Obi bisa kalaman da ya yi cewa ya damu kwarai da yadda gwamnatin APC take ci gaba da kinkimo bashi a gida waje.

A dai cikin wannan makon ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ya nuna damuwarsa kan yadda gwamnatin APC ke ci gaba da ciyo wa ‘yan Nijeriya bashi a shafinsa na twitter. “A sulusin farko na 2023, ana bin Nijeriya bashin naira tiriliyan 87.9, inda aka samu karin naira tiriliyan 10 a karshen shekarar 2023. Wannan babban abun takaici ne kuma ya kamata gwamnatin APC ta nemo hanyar warware lamura ba ta hanyar bashi ba,” in ji Obi.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

A martanin nasa, Onanuga ya ci gaba da cewa gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ba ta damuwa ko mayar da hankali kan Peter Obi da magoya bayansa.

Mashawarcin ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da yin aiki tukuru ba tare da damuwa da zargin ‘yan adawa ba.

“A yanzu haka, mun mayar da hankali kan gudanar da harkokin gwamnati kuma ba mu son a karkatar da hankalinmu kan abin da gwamnati ta saka gaba a kai. A kowani lokaci muna cikin aiki ba mu ko kallon ‘yan adawa masu suka.

“Abin da na sani game da yakin neman zaben Peter Obi shi ne, a karon farko a tarihin siyasar Nijeriya mun sami dan takara da ya bijiro da tsattsauran ra’ayin kabilanci da addini wanda ya yi amfani da su domin cin zabe. Wadannan abubuwa guda biyu suna da matukar hatsari a cikin siyasar Nijeriya.

“Lallai wadannan abubuwa guda biyu suna da matukar tsari ga siyasar Nijeriya a halin yanzu,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Baya Ta Haihu: INEC Ta Rushe Babban Taron Jam’iyyar LP Na Kasa

Next Post

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 week ago
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 week ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 week ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

2 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

2 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

2 weeks ago
Next Post
PDP

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

LABARAI MASU NASABA

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

Kantoma Na Ƙaramar Hukumar Shira Ya Rasu Kwanaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi

May 12, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.