ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyu Masu Hatsari Da Peter Obi Ya Haddasa A Siyasar Nijeriya –Fadar Shugaban Kasa

•Ku Nemo Hanyar Warware Bashin Da Kuke Lafta Wa Nijeriya - Obi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
peter

Fadar shugaban kasa ta zargi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi bisa shigo da wasu abubuwa guda biyu masu hatsari a cikin siyasar Nijeriya a zaben da ya gabata.

Mashawarcin shugaban kasa, Bayo Onanuga, shi ne ya zargi Peter Obi da shigo da addini da kabilanci cikin siyasar Nijeriya a lokacin zaben 2023.

  • Mun Dukufa Magance Matsalolin Bangaren Lantarki, In Ji Minista
  • Yadda Musulmi Ke Shirye-shiryen Bikin Karamar Sallah Cikin Tsadar Rayuwa

Mashawarcin shugaban kasan ya bayyana hakan ne a wani shirin gidan rediyo tare da Seun Okinbaloye, inda ya tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta mayar da hankali kan abubuwan da ta sa a gaba na ci gaba ba damuwa da maganganun ‘yan adawa ba.

ADVERTISEMENT

Onanuga Ya bayyana hakan ne domin mayar da martini ga Peter Obi bisa kalaman da ya yi cewa ya damu kwarai da yadda gwamnatin APC take ci gaba da kinkimo bashi a gida waje.

A dai cikin wannan makon ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi ya nuna damuwarsa kan yadda gwamnatin APC ke ci gaba da ciyo wa ‘yan Nijeriya bashi a shafinsa na twitter. “A sulusin farko na 2023, ana bin Nijeriya bashin naira tiriliyan 87.9, inda aka samu karin naira tiriliyan 10 a karshen shekarar 2023. Wannan babban abun takaici ne kuma ya kamata gwamnatin APC ta nemo hanyar warware lamura ba ta hanyar bashi ba,” in ji Obi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

A martanin nasa, Onanuga ya ci gaba da cewa gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ba ta damuwa ko mayar da hankali kan Peter Obi da magoya bayansa.

Mashawarcin ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da yin aiki tukuru ba tare da damuwa da zargin ‘yan adawa ba.

“A yanzu haka, mun mayar da hankali kan gudanar da harkokin gwamnati kuma ba mu son a karkatar da hankalinmu kan abin da gwamnati ta saka gaba a kai. A kowani lokaci muna cikin aiki ba mu ko kallon ‘yan adawa masu suka.

“Abin da na sani game da yakin neman zaben Peter Obi shi ne, a karon farko a tarihin siyasar Nijeriya mun sami dan takara da ya bijiro da tsattsauran ra’ayin kabilanci da addini wanda ya yi amfani da su domin cin zabe. Wadannan abubuwa guda biyu suna da matukar hatsari a cikin siyasar Nijeriya.

“Lallai wadannan abubuwa guda biyu suna da matukar tsari ga siyasar Nijeriya a halin yanzu,” in ji shi.

peter
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
PDP

Shugabancin PDP: Yankin Arewa Ta Tsakiya Ya Dage Kan Cika Wa’adin Ayu

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.