• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

by Abubakar Sulaiman
6 days ago
in Labarai
0
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban riƙon ƙwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Sanata David Mark, ya bayyana jam’iyyar a matsayin wata hanya da za a bi don cimma haɗin kan Arewa, da cigaba da kawo ci gaban yankin. Ya bayyana haka ne a jawabin buɗe taro na uku na babbar ganawar ƙungiyar tuntuɓa a siyasa (NPCG) ta Arewa, a Abuja.

Taron wanda ya gudana bayan bayyana ADC a matsayin sabon dandalin siyasa ga wasu fitattun ‘yan adawa gabanin zaɓen 2027, ya nemi hanyoyin da za a bi wajen haɗa kan al’ummar Arewa. A taro na baya, ƙungiyar NPCG ƙarƙashin jagorancin tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ta bukaci a gaggauta bayyana wata sabuwar jam’iyya domin kare muradun yankin.

  • ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?
  • Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

A cewar Sanata Mark, Arewa na cikin wani hali mai sosa rai, yana mai jaddada cewa ‘yan Arewa su ne za su iya magance matsalolin da ke damun su. Ya buƙaci a guji maganganu masu tayar da fitina da siyasar rarrabuwa, tare da mayar da hankali kan muhimman ayyuka kamar ilimi, da kiwon lafiya da ababen more rayuwa.

Sanata Mark ya bayyana cewa duk da albarkatun ƙasa, arziƙin noma, da yawan al’adu, Arewa na fama da matsaloli da suka haɗa da rashin tsaro, talauci, rikice-rikicen ƙabilanci da na addini, da kuma gazawar ci gaban tattalin arziki da siyasa. Ya bayyana yadda rashin tsaro ke hana masu zuba jari shiga yankin, wanda ke ƙara ƙarfafa fatara da laifuka.

Ya koka kan yadda ake amfani da ƙabilanci da addini wajen haifar da rikice-rikice don biyan buƙatun wasu. Ya buƙaci al’umma su koma ga zaman lafiya da juna da suka yi fice da shi a baya, inda kalmar “Ɗan Arewa” ke bayyana duƙulalliyar halayyarsu. Mark ya jaddada cewa ADC za ta kawo bambanci, domin a wajensu siyasa ibada ce, ba hanya ta yaudara ba. Ya ƙara da cewa dole ne Arewa ta farka daga wannan yanayi, domin a da yankin ne mafi aminci a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCArewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Next Post

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Related

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

25 minutes ago
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
Labarai

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

1 hour ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

12 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

13 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

18 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

20 hours ago
Next Post
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

LABARAI MASU NASABA

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

August 2, 2025
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

August 2, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.