• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

by Abubakar Sulaiman
4 weeks ago
in Labarai
0
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban riƙon ƙwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Sanata David Mark, ya bayyana jam’iyyar a matsayin wata hanya da za a bi don cimma haɗin kan Arewa, da cigaba da kawo ci gaban yankin. Ya bayyana haka ne a jawabin buɗe taro na uku na babbar ganawar ƙungiyar tuntuɓa a siyasa (NPCG) ta Arewa, a Abuja.

Taron wanda ya gudana bayan bayyana ADC a matsayin sabon dandalin siyasa ga wasu fitattun ‘yan adawa gabanin zaɓen 2027, ya nemi hanyoyin da za a bi wajen haɗa kan al’ummar Arewa. A taro na baya, ƙungiyar NPCG ƙarƙashin jagorancin tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ta bukaci a gaggauta bayyana wata sabuwar jam’iyya domin kare muradun yankin.

  • ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?
  • Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

A cewar Sanata Mark, Arewa na cikin wani hali mai sosa rai, yana mai jaddada cewa ‘yan Arewa su ne za su iya magance matsalolin da ke damun su. Ya buƙaci a guji maganganu masu tayar da fitina da siyasar rarrabuwa, tare da mayar da hankali kan muhimman ayyuka kamar ilimi, da kiwon lafiya da ababen more rayuwa.

Sanata Mark ya bayyana cewa duk da albarkatun ƙasa, arziƙin noma, da yawan al’adu, Arewa na fama da matsaloli da suka haɗa da rashin tsaro, talauci, rikice-rikicen ƙabilanci da na addini, da kuma gazawar ci gaban tattalin arziki da siyasa. Ya bayyana yadda rashin tsaro ke hana masu zuba jari shiga yankin, wanda ke ƙara ƙarfafa fatara da laifuka.

Ya koka kan yadda ake amfani da ƙabilanci da addini wajen haifar da rikice-rikice don biyan buƙatun wasu. Ya buƙaci al’umma su koma ga zaman lafiya da juna da suka yi fice da shi a baya, inda kalmar “Ɗan Arewa” ke bayyana duƙulalliyar halayyarsu. Mark ya jaddada cewa ADC za ta kawo bambanci, domin a wajensu siyasa ibada ce, ba hanya ta yaudara ba. Ya ƙara da cewa dole ne Arewa ta farka daga wannan yanayi, domin a da yankin ne mafi aminci a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCArewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Next Post

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Related

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

40 minutes ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 hours ago
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

3 hours ago
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru
Labarai

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

3 hours ago
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

3 hours ago
Next Post
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.