• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afirka Na Bukatar Malaman Makaranta Miliyan 15 Nan Da 2030 -Patrick

by Leadership Hausa
2 years ago
in Ilimi
0
Afirka Na Bukatar Malaman Makaranta Miliyan 15 Nan Da 2030 -Patrick
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Hukumar kula da al’amuran ilmi, kimiyya da al’adu ta majalisar dinkin duniya (UNICEF) ta bayyana cewa Afirka na bukatar Malaman makaranta a kalla milyan 15 da za su koyar a makarantun Sakandare na da shekara ta 2030.

Ya ce Afirka na fama da karancin Malaman makaranta a makarantu masu yawa al’amari ya kasance haka ne  saboda rashin isassun kudaden da ake ware ma sashen ilimi a shekarun da suka gabata.Ya ci gaba da bayanin cewa duk da cigaban da aka samu akan daukar Malaman makaranta shekaru biyar da suka wuce a nahiyar amma ya ce al’amarin ya hadu da tafiyar Hawainiya don haka ya yi kira da gwamnatocin Afirka Kudu da Sahara su kara yawan Malaman makarantar da suke dauka ko wace shekara.

  • Abubuwan Da Nijeriya Za Ta Mora Daga Taron Saudiyya Da Jamus
  • Kayan Tarihi Na Manzon Allah S.A.W (II)

Babban mai sharhi kan harkokin ilimi a UNESCO,Patrick Nkengne,ne ya bayyana Malaman makaranta ‘yan kadan ne suke kula da milyoyin dalibai a nahiyar Afirka.

Ya ci gaba da bayanin “Lokacin da ajin da ya dace da dalibai 50 amma sai aka samu 100, tun tashin farko an fi son Malamin makaranta daya ya kula da dalibai 40 zuwa 50 abin da doka tafi amincewa da shi ke nan,amma a fili abin ya nuna da akwai matsala.Yayin da ake cigaba da samu karancin azuzuwa matsalar rashi ta karu ke nan cewar Nkengne,”.

Ilimin da ya shafi Sakandaren da akwai bukatar Malaman makaranta da yawa a yawancin kasashen Afirka.Emmanuel Manyasa shi ma kwararre ta harkar ilimi ya ce makarantu da yawa suna yaye daliban da basu da ilimi ne saboda rashin kwararrun Malaman makaranta.

“Wannan ya nuna da akwai Malamai wadanda basu jin dadi tsanin saboda su kansu da kuma masu koyo.

Masu koyo basu samun kulawar da ta kamata su samu,ya yin da su Malaman makaranta yawan daliban da suke kulawa da su ya dame su da yawan awoyin da suke dauka na koyarwa wanda hakan bai basu dama ta shirya abubuwan da za su koya wa dalibai.Shi yasa suke zuwa aji ba tare da sun shirya ba tare da danne  wata dama data kamata su samu.Daga karshe sai makarantu su zama wurin zuwa a koya ba tare da karuwa da ilimin daya dace a samu ba.”

Kamar yadda Nkengne ya ce a kasashen da suke da isassun Malaman makaranta su makarantun ne suke kokarin bada ilimi mai nagarta ka wadanda suke koyo saboda rashin samun kyakkyawan farawa ta ilimin da ya dace a fara sani.

“Abu mafi dacewa shi ne ace Malamin makaranta ya samu shirin yadda zai fuskanci dalibai wajen koya masuIn saboda hakan za isa su karu da ilimi mai inganci.Sai dai kash! Kuma wadanda za su koyar din basu samu kwarewa akan darussan da suka kamata su koyar.

“A irin wannan yanayin ba yadda za ayi su daliban su koyi wani abin azo a gani saboda basu da Malami,wannan abin yana da wuyar ganewa idan ana bukatar yin hakan abu mafi dacewa shi ne su Malaman ya dace  ay masu jarabawa da tabbatar da sun samu nasarar data su koyar.”

Manyasa ya ce ya kamata a karfafawa Malaman makaranta gwiwa domin hakan zai sa su maida hankali wajen ganin an cimma burin da ake bukata.

Ya kara jaddada cewa “Ya kamata mu tabbatar da ana kai Malaman makaranta wuraren da suka kamata a fadin kasa.Ta haka ne ake gane me ya dace ayi yaya za ayi shi na jan hakalin su Malaman su yi aiki a wuraren da basu taba tunanin za su je ba.

Yawancinsu ba su shirya ma wurin da yanayin shi basu saba da shi ba ga kuma al’amarin da ya shafi rashin tsaro,ko zuwa kauye su yi aiki,ai zai yi wuyar a shawo kan irin kan wadancan Malaman su je su yi aiki a irin wadancan wuraren? Ai wannan al’amari ne mai muhimmanci.”

Masu ruwa da tsaki shi yasa suka ja hankalin gwamnatocin Afirka su duba ko tunanin Malaman makaranta nawa za a bukata nan dka shekaru goma masu zuwa,ga kuma duba yadda za a rika horar da su,da samar da kudade saboda daukar Malamn tare da horar da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shari’ar Zaben Kano: Alhaki Kwikwiyo

Next Post

Hanyoyin Warware Kalubalen Da Kiwon Kifi Ke Fuskanta A Nijeriya

Related

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

3 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

3 days ago
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
Ilimi

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

3 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

1 week ago
Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
Ilimi

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

2 weeks ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

4 weeks ago
Next Post
Hanyoyin Warware Kalubalen Da Kiwon Kifi Ke Fuskanta A Nijeriya

Hanyoyin Warware Kalubalen Da Kiwon Kifi Ke Fuskanta A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.