• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce aikin shimfiɗa bututun gas daga Ajaokuta-Kaduna-Kano (AKK) zai bunƙasa hanyoyin tattalin arzikin Arewacin Nijeriya.

A takardar sanarwa ga manema labarai da ya rattaba wa hannu, mai ba ministan shawara kan aikin jarida, Malam Rabiu Ibrahim, ya ce, Idris ya bayyana haka ne a Kaduna a lokacin da ya kai ziyara wurin aikin bututun gas na AKK da ake yi a gaɓar Kogin Kaduna.

  • Yadda Aka Kashe Mutum Shida Da Sace Wasu Ranar Sallah A Sokoto
  • Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir

Ya halarci wurin ne tare da rakiyar Ministan Kuɗi, Wale Edun; da Ƙaramin Ministan Albarkatun Gas, Mista Ekperikpe Ekpo, da kuma Shugaban Kamfanin NNPC, Mele Kyari.

A jawabinsa a wajen ziyarar, Idris ya ce, “Aikin na AKK ya mayar da hankali ne wajen fitar da ɗimbin ƙarfin tattalin arzikin Arewacin Nijeriya. Gas ɗin da za a yi jigilarsa zai samar da makamashin da ake buƙata ga gidaje, kasuwanci, da masana’antu, sannan kuma zai ba da damar hada-hadar sufuri da rage farashin sa.

“Ci gaba da aiwatar da wannan aiki, wanda shi ne babban aikin bututun gas na cikin gida a Nijeriya zuwa yanzu, wanda gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta yi, wata alama ce da ke nuni da ƙudirin Shugaban Ƙasa na bunƙasa masana’antu da ci gaban tattalin arzikin kowane ɓangare na ƙasar nan.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

Haka kuma ya yaba da aikin a matsayin mai muhimmanci ga cigaban masana’antu da tattalin arzikin Nijeriya a ƙarƙashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana shi a matsayin aikin bututun gas na cikin gida mafi girma a ƙasar.

Ministan ya kuma danganta cigaban tattalin arziki da tsaro, inda ya ce yawancin matsalolin tsaro da ake fama da su a Arewacin Nijeriya suna faruwa ne sakamakon taɓarɓarewar tattalin arziki, wanda za a iya ragewa ta hanyar samar da ayyukan yi da bunƙasa tattalin arziƙi.

Ya ce, “Samar da makamashi a gidaje, gonaki, da masana’antu ya na da matuƙar muhimmanci ga samar da ayyukan yi masu yawa.”

Idris ya bayyana yiwuwar aikin zai taimaka wa harkar noma sosai a Arewacin Nijeriya.

Bugu da ƙari, ya yi nuni da irin tasirin da irin waɗannan ayyuka ke yi a faɗin ƙasar nan, inda ya ce a watan da ya gabata an ƙaddamar da wasu muhimman ayyukan samar da gas guda uku a yankin Neja Delta.

Ya ƙara da cewa aikin na AKK zai tallafa wa Shirin Shugaban Ƙasa na Gas (Pi-CNG), wanda tuni ya jawo jarin sama da dalar Amurka miliyan 50.

Ya ce, “Aikin bututun na AKK wani ginshiƙin fata ne, wanda zai farfaɗo da tattalin arzikin dukkan ‘yan Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AkkCNGKRPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (2)

Next Post

Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

Related

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

47 minutes ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

1 hour ago
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

5 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

7 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

20 hours ago
Next Post
Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.