• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kautal Hore, Bodejo A Gaban Kotu Kan Zargin Ta’addanci

by Muhammad
2 years ago
Miyetti

Gwamnatin Nijeriya ta gurfanar da shugaban kungiyar Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Bodejo a gaban kotu kan zargin aikata laifukan ta’addanci.

An gurfanar da Bodejo a gaban wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja kan zarginsa da kafa da kuma tallafa wa kungiyar ‘yan bindiga ta ‘Kungiya Zaman Lafiya’ ba bisa ka’ida ba.

  • ‘Yansanda Sun Kama Shugaban Kungiyar Miyetti-Allah A Adamawa
  • Ba Mu Kama Shugaban Miyetti Allah Ba – DSS

An gurfanar da Bodejo ne a ranar Juma’a a kan tuhume-tuhume guda uku da ofishin babban mai shari’a na kasa ya shigar, inda ake tuhumarsa da karya dokar ta’addanci ta shekarar 2022.

Bodejo ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da ake yi masa a lokacin da aka karanto masa tuhumar a gaban kotu, daga nan ne mai shari’a Inyang Ekwo ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare shi a hannun hukumar leken asiri ta DIA.

Mai shari’a Ekwo ya dage ci gaba da sauraron shari’ar har zuwa ranar 27 ga watan Mayun 2024.

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

Idan za ku tuna kwanakin bayan an kama shugaban na Miyetti Allah a jihar Nasarawa, bayan kungiyar ta kaddamar da wata kungiyar ‘yan banga mai suna Kungiyar Zaman Lafiya.

A lokacin bikin kaddamar da kayan Fulani na mutum 1,144 a ranar 17 ga watan Junairu, 2024, Bodejo ya ce, an dauki wannan matakin ne don magance matsalar ‘yan fashi da satar shanu da ma duk wani nau’in rashin tsaro da yake addabar jihar Nasarawa.

Bayan kama shi, shugaban na Miyetti Allah, ya shigar da kara a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja domin kalubalantar tsare shi da aka yi.

A martanin da babban Lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi (SAN), a ranar 5 ga watan Fabrairu, ya shigar da kara a gaban kotu, inda ya bukaci a ci gaba da tsare Bodejo har sai an kammala bincike tare da gurfanar da shi a gaban kotu.

Mai shari’a Inyang Ekwo, wanda ke sauraron karar Bodejo, ya bai wa gwamnatin tarayya izinin tsare shi na tsawon kwanaki 15 a hannun hukumar leken asiri ta tsaro.

Daga bisani, alkalin ya umurci gwamnatin tarayya da ta gurfanar da shugaban na Miyetti Allah, ko kuma ta sake shi ya ci gaba da harkokinsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa
Manyan Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Next Post
Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

Ɗaliban Jami'ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.