ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kautal Hore, Bodejo A Gaban Kotu Kan Zargin Ta’addanci

by Muhammad
2 years ago
Miyetti

Gwamnatin Nijeriya ta gurfanar da shugaban kungiyar Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Bodejo a gaban kotu kan zargin aikata laifukan ta’addanci.

An gurfanar da Bodejo a gaban wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja kan zarginsa da kafa da kuma tallafa wa kungiyar ‘yan bindiga ta ‘Kungiya Zaman Lafiya’ ba bisa ka’ida ba.

  • ‘Yansanda Sun Kama Shugaban Kungiyar Miyetti-Allah A Adamawa
  • Ba Mu Kama Shugaban Miyetti Allah Ba – DSS

An gurfanar da Bodejo ne a ranar Juma’a a kan tuhume-tuhume guda uku da ofishin babban mai shari’a na kasa ya shigar, inda ake tuhumarsa da karya dokar ta’addanci ta shekarar 2022.

ADVERTISEMENT

Bodejo ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da ake yi masa a lokacin da aka karanto masa tuhumar a gaban kotu, daga nan ne mai shari’a Inyang Ekwo ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare shi a hannun hukumar leken asiri ta DIA.

Mai shari’a Ekwo ya dage ci gaba da sauraron shari’ar har zuwa ranar 27 ga watan Mayun 2024.

LABARAI MASU NASABA

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Idan za ku tuna kwanakin bayan an kama shugaban na Miyetti Allah a jihar Nasarawa, bayan kungiyar ta kaddamar da wata kungiyar ‘yan banga mai suna Kungiyar Zaman Lafiya.

A lokacin bikin kaddamar da kayan Fulani na mutum 1,144 a ranar 17 ga watan Junairu, 2024, Bodejo ya ce, an dauki wannan matakin ne don magance matsalar ‘yan fashi da satar shanu da ma duk wani nau’in rashin tsaro da yake addabar jihar Nasarawa.

Bayan kama shi, shugaban na Miyetti Allah, ya shigar da kara a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja domin kalubalantar tsare shi da aka yi.

A martanin da babban Lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi (SAN), a ranar 5 ga watan Fabrairu, ya shigar da kara a gaban kotu, inda ya bukaci a ci gaba da tsare Bodejo har sai an kammala bincike tare da gurfanar da shi a gaban kotu.

Mai shari’a Inyang Ekwo, wanda ke sauraron karar Bodejo, ya bai wa gwamnatin tarayya izinin tsare shi na tsawon kwanaki 15 a hannun hukumar leken asiri ta tsaro.

Daga bisani, alkalin ya umurci gwamnatin tarayya da ta gurfanar da shugaban na Miyetti Allah, ko kuma ta sake shi ya ci gaba da harkokinsa.

Miyetti
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
Manyan Labarai

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

Ɗaliban Jami'ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.