• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gurfanar Da Wata Mata A Gaban Kuliya Bisa Zargin Damfarar Wani Kamfani N350m

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
9 months ago
in Tsaro
0
Kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Legas, a ranar Talata, ta gurfanar da wata mata mai suna Rukayya Dantata ‘yar shekaru 35 a gaban kuliya bisa zargin damfarar wani kamfanin tuntuba na Bureau de Change kudi Naira miliyan 350,900,000.

 

An gurfanar da Dantata a gaban kotun laifuffuka ta musamman da ke Ikeja da laifuffuka biyu da suka hada da zamba, damfara da kuma karbar kudi ta hanyar karya.

  • EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Taraba Ishaku Kan Zargin Badaƙalar 27bn
  • Rahoto Ya Nuna Yadda Noma Ya Samu Koma-baya A Nijeriya

Lauyan mai shigar da kara, Ezekiel Rimamsomte, ya shaida wa kotun cewa Dantata ta aikata laifukan da ake zarginsa tsakanin watan Yuli zuwa Agustan 2022.
Ya ce wacce ake kara ta samu Naira miliyan 350,900,000 ta hanyar damfara, inda aka tura ta zuwa asusunta na Zenith Bank, 2082551256, da kuma asusun kamfaninta mai suna Adat Bentures’ mai lamba, 1014937041, da sunan Rukayya Saadina Dantata.

Rimamsomte ta kara da cewa Dantata ta yaudari wadanda masu kudin, Saka Rasak na Rosiyike, da wasu na kamafanin Financial Consultant Ltd, da ke No. 50 Kingsway Building, Legas, ta hanyar yin kamar suna gudanar da harkokin kasuwanci na halal.
A cewarta, laifukan da aka aikata sun ci karo da sashe na 1 (a) (3) na dokar damfara da sauran laifukan da suka shafi doka ta 2006, da sashe na 323 na dokar laifuka ta Jihar Legas 2015.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Sai dai Dantata ya musanta zargin da ake mata.

Igbodo ya bukaci kotun da ta bayar da belin wacce ake tuhuma a karkashin “mafi sassaucin sharuda,” yana mai cewa, “Wanda ake tuhumar ya bi dukkan sammacin ‘yansanda da Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arziki Ta’annati, kuma ba ta tsallake beli ba, duk da kalubalen lafiyarta.”

Ya kuma shaida wa kotun cewa mijin Dantata, Alhaji Ismaih Singer, da kuma wata Otunba Olutaye Ariyo sun hallara a gaban kotu domin a ba ta belinta.

Mai gabatar da kara bai musanta da neman belin ba kuma ya bar hukuncin ga hukuncin kotun.

A wani takaitaccen hukunci mai shari’a Rahmon Oshodi ya bayar da belin Dantata kan kudi Naira miliyan 30 tare da mutane biyu da za su tsaya mata.

Alkalin ya bayyana cewa, “Dukkanin wadanda za su tsaya mata dole ne su ba da takardar shaidar biyan haraji na shekaru uku ga gwamnatin Jihar Legas.”

Mai shari’a Oshodi ya kuma umurci Dantata da ta ajiye fasfo dinta da sauran takardun tafiya zuwa ga babban magatakardar kotun, inda ya kara da cewa dole ne magatakardar ta tantance adireshin gidanta da ofishinta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

FIFA Ta Dakatar Da Martinez Daga Buga Wasanni Biyu

Next Post

Xi Ya Yi Kira Ga Ma’aikatan Masana’antu Da Su Ba Da Gudummawar Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin

Related

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

5 days ago
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
Tsaro

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

1 week ago
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

2 weeks ago
Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato
Tsaro

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

2 weeks ago
Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
Tsaro

Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina

3 weeks ago
Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje

3 weeks ago
Next Post
Xi Ya Yi Kira Ga Ma’aikatan Masana’antu Da Su Ba Da Gudummawar Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Ma’aikatan Masana’antu Da Su Ba Da Gudummawar Farfado Da Arewa Maso Gabashin Sin

LABARAI MASU NASABA

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

July 2, 2025
Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.