• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Jinjina Wa Tawagar NPA Kan Samun Nasarar Sayar Da Danyen Mai Da Takardar Naira

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
in Tattalin Arziki
0
Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Karamin Kwamitin Fasaha na wanzar da tsarin Gwamnatin Tarayya na dayen mai da ake sayarwa na cikin gida da kayan da ake sarrafawa a kan takardar Naira Zacch Adedeji, ya jinjiawa tawagar shirin sayen kaya wato (OSS) wadda Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ke jagorantar tabbatar an gudanar da ayyukan a cikin nasara.

Adedeji wanda kuma shi ne, Shugaban Hukumar tara Haraji ta kasa ya ya yi wannan yabon ne, a lokacin da ya kai ziyarar aiki a shalkawatar Hukumar NPA a ranar Alhamis da ta gabata.

  • Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda A Zamfara

Kazalika, Adedeji, ya godewa, tawagar ta Hukumar NPA, kan irin gudunmawar da take bayarwa wajen wanzar da umarnin na fadara shugaban kasa na ayyukan sayar da danyen man a cikin gida Nijeriya da kuma sauran kayan da ake sararafwa kan takardar Naira

Adedeji ya kara da cewa,“Mun lura da namijin kokarin da tawagar ke kan yi wajen samun nasarar gudanar da ayyukan, wanda hakan ya kuma nuna irin kishin kasar da tawagar take da shi, na son cimma nasara”.

Ya ci gaba da cewa,“ A saboda haka, muna karawa tawagar kwarin guiwar da su kara zagewa da kuma mayar da hankali domin a samu cimma nasarar gudanar da shirin.”

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

Adedeji ya ce,“ Muna mika godiyar mu ga sauran hukumomi da suke a cikin wannan aikin, saboda irin dimbin goyon baya da hadin kai da suka bayarwa”.

Da yake mayar da na sa bayanin, Babban Manajin Darakta na Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, “ Wannan yabon da Kwamitin ya yiwa tawagar, zai karawa tawagar kwarin guiwa ne, wajen kara mayar da hankali kan shirin”.

Dakta Dantsoho ya kuma yi amfani da damar wajen yabawa ministan Tattalin Arziki na Albarkatun Ruwa Hon. Adegboyega Oyetola a kan samar da sahihin shuganaci na gari, wanda hakan ya taimaka, wajen samun cin nasarar shirin.

“Muna godewa namjin kokarin Shugaban Karamin Kwamitin Zacch Adedeji, musamman kan goyon bayan da yake bayarwa har ta kai ga, shirin ya samu cimma wannan nasarar”.

Kazalika, Dakta Dantsoho, ya bayya cewa, bisa samar da wannan shirin, na sayar da danyen man kan takardar Naira da kuma kayan da ake sarrafawa a cikin Nijeriya, hakan ya nuna yadda Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya taimaka wajen ragewa Nijeriya yin asarar biliyoyin Naira.

Dakta Dantsoho ya kara da cewa, hakan ya kuma bayar da wata dama na kula da fannin makamashi na kasar, kara zurafafa cinikayya, samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya, damar rage karancin albarkatun man fetur da kuma kawo karashen jerin Gwanonin layukan ababen hawa a gidajen sayar da man fetur na kasar, musamman a wannan lokutan na bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

Wannan shirin dai na zuwa ne, daidai lokacin da matatar man fetur ta Dangote, ta rage farashin man da take samarwa samfarin PMS zuwa Naira 899.50 na kowacce lita daya,

Sauran tawagar da ke a cikin Kwamtin sun hada da Hukumomin NIMASA, NMDPRA, NUPRC, NEPZA, FIRS, NNPC, DAPMAN, IPMAN, PHS, MEMAN, NDLEA, Matatar Dangote, Kwantirola na Kwastam da kuma Hafsan Rundunar Sojin Sama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fiye Da Kaso 80 Na Kamfanonin Sin Sun Fadada Zuba Jari A Waje A 2024

Next Post

Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

Related

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 week ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

2 weeks ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

3 weeks ago
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Tattalin Arziki

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

3 weeks ago
Next Post
Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

May 12, 2025
Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

May 12, 2025
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

May 12, 2025
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

May 12, 2025
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 12, 2025
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

May 12, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

May 12, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno

May 12, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur

May 12, 2025
 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

 Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.