• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Jinjina Wa Tawagar NPA Kan Samun Nasarar Sayar Da Danyen Mai Da Takardar Naira

by Abubakar Abba and Sulaiman
10 months ago
Gaza

Shugaban Karamin Kwamitin Fasaha na wanzar da tsarin Gwamnatin Tarayya na dayen mai da ake sayarwa na cikin gida da kayan da ake sarrafawa a kan takardar Naira Zacch Adedeji, ya jinjiawa tawagar shirin sayen kaya wato (OSS) wadda Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ke jagorantar tabbatar an gudanar da ayyukan a cikin nasara.

Adedeji wanda kuma shi ne, Shugaban Hukumar tara Haraji ta kasa ya ya yi wannan yabon ne, a lokacin da ya kai ziyarar aiki a shalkawatar Hukumar NPA a ranar Alhamis da ta gabata.

  • Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda A Zamfara

Kazalika, Adedeji, ya godewa, tawagar ta Hukumar NPA, kan irin gudunmawar da take bayarwa wajen wanzar da umarnin na fadara shugaban kasa na ayyukan sayar da danyen man a cikin gida Nijeriya da kuma sauran kayan da ake sararafwa kan takardar Naira

Adedeji ya kara da cewa,“Mun lura da namijin kokarin da tawagar ke kan yi wajen samun nasarar gudanar da ayyukan, wanda hakan ya kuma nuna irin kishin kasar da tawagar take da shi, na son cimma nasara”.

Ya ci gaba da cewa,“ A saboda haka, muna karawa tawagar kwarin guiwar da su kara zagewa da kuma mayar da hankali domin a samu cimma nasarar gudanar da shirin.”

LABARAI MASU NASABA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

Adedeji ya ce,“ Muna mika godiyar mu ga sauran hukumomi da suke a cikin wannan aikin, saboda irin dimbin goyon baya da hadin kai da suka bayarwa”.

Da yake mayar da na sa bayanin, Babban Manajin Darakta na Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, “ Wannan yabon da Kwamitin ya yiwa tawagar, zai karawa tawagar kwarin guiwa ne, wajen kara mayar da hankali kan shirin”.

Dakta Dantsoho ya kuma yi amfani da damar wajen yabawa ministan Tattalin Arziki na Albarkatun Ruwa Hon. Adegboyega Oyetola a kan samar da sahihin shuganaci na gari, wanda hakan ya taimaka, wajen samun cin nasarar shirin.

“Muna godewa namjin kokarin Shugaban Karamin Kwamitin Zacch Adedeji, musamman kan goyon bayan da yake bayarwa har ta kai ga, shirin ya samu cimma wannan nasarar”.

Kazalika, Dakta Dantsoho, ya bayya cewa, bisa samar da wannan shirin, na sayar da danyen man kan takardar Naira da kuma kayan da ake sarrafawa a cikin Nijeriya, hakan ya nuna yadda Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya taimaka wajen ragewa Nijeriya yin asarar biliyoyin Naira.

Dakta Dantsoho ya kara da cewa, hakan ya kuma bayar da wata dama na kula da fannin makamashi na kasar, kara zurafafa cinikayya, samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya, damar rage karancin albarkatun man fetur da kuma kawo karashen jerin Gwanonin layukan ababen hawa a gidajen sayar da man fetur na kasar, musamman a wannan lokutan na bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

Wannan shirin dai na zuwa ne, daidai lokacin da matatar man fetur ta Dangote, ta rage farashin man da take samarwa samfarin PMS zuwa Naira 899.50 na kowacce lita daya,

Sauran tawagar da ke a cikin Kwamtin sun hada da Hukumomin NIMASA, NMDPRA, NUPRC, NEPZA, FIRS, NNPC, DAPMAN, IPMAN, PHS, MEMAN, NDLEA, Matatar Dangote, Kwantirola na Kwastam da kuma Hafsan Rundunar Sojin Sama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.