• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Jinjina Wa Tawagar NPA Kan Samun Nasarar Sayar Da Danyen Mai Da Takardar Naira

by Abubakar Abba and Sulaiman
8 months ago
in Tattalin Arziki
0
Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Karamin Kwamitin Fasaha na wanzar da tsarin Gwamnatin Tarayya na dayen mai da ake sayarwa na cikin gida da kayan da ake sarrafawa a kan takardar Naira Zacch Adedeji, ya jinjiawa tawagar shirin sayen kaya wato (OSS) wadda Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ke jagorantar tabbatar an gudanar da ayyukan a cikin nasara.

Adedeji wanda kuma shi ne, Shugaban Hukumar tara Haraji ta kasa ya ya yi wannan yabon ne, a lokacin da ya kai ziyarar aiki a shalkawatar Hukumar NPA a ranar Alhamis da ta gabata.

  • Zargin China Da Bautar Da Leburori a Gonar Tumatir a Xinjiang: Mene Ne Gaskiyar Lamarin?
  • Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda A Zamfara

Kazalika, Adedeji, ya godewa, tawagar ta Hukumar NPA, kan irin gudunmawar da take bayarwa wajen wanzar da umarnin na fadara shugaban kasa na ayyukan sayar da danyen man a cikin gida Nijeriya da kuma sauran kayan da ake sararafwa kan takardar Naira

Adedeji ya kara da cewa,“Mun lura da namijin kokarin da tawagar ke kan yi wajen samun nasarar gudanar da ayyukan, wanda hakan ya kuma nuna irin kishin kasar da tawagar take da shi, na son cimma nasara”.

Ya ci gaba da cewa,“ A saboda haka, muna karawa tawagar kwarin guiwar da su kara zagewa da kuma mayar da hankali domin a samu cimma nasarar gudanar da shirin.”

Labarai Masu Nasaba

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Adedeji ya ce,“ Muna mika godiyar mu ga sauran hukumomi da suke a cikin wannan aikin, saboda irin dimbin goyon baya da hadin kai da suka bayarwa”.

Da yake mayar da na sa bayanin, Babban Manajin Darakta na Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho ya bayyana cewa, “ Wannan yabon da Kwamitin ya yiwa tawagar, zai karawa tawagar kwarin guiwa ne, wajen kara mayar da hankali kan shirin”.

Dakta Dantsoho ya kuma yi amfani da damar wajen yabawa ministan Tattalin Arziki na Albarkatun Ruwa Hon. Adegboyega Oyetola a kan samar da sahihin shuganaci na gari, wanda hakan ya taimaka, wajen samun cin nasarar shirin.

“Muna godewa namjin kokarin Shugaban Karamin Kwamitin Zacch Adedeji, musamman kan goyon bayan da yake bayarwa har ta kai ga, shirin ya samu cimma wannan nasarar”.

Kazalika, Dakta Dantsoho, ya bayya cewa, bisa samar da wannan shirin, na sayar da danyen man kan takardar Naira da kuma kayan da ake sarrafawa a cikin Nijeriya, hakan ya nuna yadda Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya taimaka wajen ragewa Nijeriya yin asarar biliyoyin Naira.

Dakta Dantsoho ya kara da cewa, hakan ya kuma bayar da wata dama na kula da fannin makamashi na kasar, kara zurafafa cinikayya, samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya, damar rage karancin albarkatun man fetur da kuma kawo karashen jerin Gwanonin layukan ababen hawa a gidajen sayar da man fetur na kasar, musamman a wannan lokutan na bukukuwan Kirsimeti da na sabuwar shekara.

Wannan shirin dai na zuwa ne, daidai lokacin da matatar man fetur ta Dangote, ta rage farashin man da take samarwa samfarin PMS zuwa Naira 899.50 na kowacce lita daya,

Sauran tawagar da ke a cikin Kwamtin sun hada da Hukumomin NIMASA, NMDPRA, NUPRC, NEPZA, FIRS, NNPC, DAPMAN, IPMAN, PHS, MEMAN, NDLEA, Matatar Dangote, Kwantirola na Kwastam da kuma Hafsan Rundunar Sojin Sama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fiye Da Kaso 80 Na Kamfanonin Sin Sun Fadada Zuba Jari A Waje A 2024

Next Post

Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

Related

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
Tattalin Arziki

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

3 days ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

1 week ago
Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta
Tattalin Arziki

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa
Tattalin Arziki

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

2 weeks ago
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
Tattalin Arziki

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

3 weeks ago
Dangote
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

4 weeks ago
Next Post
Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

Manyan Bankunan Kasa Na Sin Da Nijeriya Sun Sabunta Yarjejeniyar Musayar Kudi

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.