Isa Abdullahi Gidan Bakko">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

An Kaddamar Da Shugabannin Kungiyar ’Yan Katako A Sabon Garin Zariya

by Isa Abdullahi Gidan Bakko
January 20, 2021
in RIGAR 'YANCI
3 min read
Kungiyar ’Yan Katako
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A makon jiya ne aka kaddamar da sabbin shugabannin kungiyar ‘yan katako reshen babbar kasuwar ‘yan katako da Sabon garin Zariya, da taron kaddamar da sabbin shugabannin ya sami halartar wakilan shugabannin ‘yan kasuwar Sabon gari da manya da kuma kananan ‘yan kasuwa da suka fito daga sassan Jihar Kaduna.

Sabbin shugabannin da aka zaba sun hada da kujerar shugaban kungiyar aka zabi tsohon matakin shugaban kungiyar Alhaji Suleiman Yusuf, wanda aka fi sani da sunan na Hari, mai Allah, sai matakin shugaba aka zabi Alhaji Lawal Garba sai babban sakataren kungiyar aka zabi Muhammed Gali sai kujerar ma’ajin kungiyar, aka zabi Alhaji Shehu Ahmed da aka fi sani da magani, sai sakataren kudi, aka zabi BilyaminiSani sai kuma sakataren tysare – tsaren kungiyar aka zabi Alhaji Ibrahi Ahmed.

samndaads

Sauran shugabannin kungiyar da aka zaba sun hada da Alhaji Shehu Hassan Baba, a matsayin jami’in watsa labarai na kungiyar, sai jami’in walwala aka zabi Jabir Hassan, sai Yusuf Yunusa a matsayin jami’in watsa labarai, sai babban jami’in watsa labarai da aka zabi, Malam Musa Yakubu, sai jami’in ladabtarwa aka zabi, Alhaji Aliyu Abdullahi, sai mai shari’a a wannan kungiyar aka zabi Alhaji Salisu Mhammed da kuma Alhaji Mohmud Garba Hasan aka zabe shi a kujerar babban jami’in kula da lafiyar shugabanni da kuma sauran ‘ya’yan kungiya, aka zabiAlhaji Mohammed Garba.

A dai lokacin kaddamar da shugannin an zabiAlhaji Aminu Abdullahi a matsayin Jami’in tsaro na wannan kungiya sai mai binciken lalitar kungiyar aka zabi Alhaji Haliru Baba.

Injiniya Mohammed Usman da kansila a wannan karmar hukuma Alhaji Yakubu Furodusa ya wwakilce a wajen taron, ya kira ga sabbin shugabannin da aka kaddanar da su kasance ma su tunanin wadanda suka zabe su, musamman ta tsara wasu hanyoyin da za su aiwatar mambobin kungiyar su amfana ta hanyoyin sana’arsu da kuma iyalansu.

Alhaji Uwaisu wanda ya wakiulci shugaban kungiyar ‘yan kasuwa na babbar kasuwar Sabon gari, Alhaji Ibrahim mai gwal, shi ma ya nuna matukar jin dadinsa na yadda kafintoci suka hada kansu tare da kafa wannan kungiyar, a cewarsa, babbr kungiyar ‘yan kasuwa ta karamar hukumar Sabon gari, bisa jagoranci Alhaji Ibrahim mai gwal, su na shirye ako wane lokaci, na ganin sun bayar da gudunmuwar day a dace ga mambobin wannan kungiyar, ta yadda mambobin za su furta cewar, sun yi murna da zaben Nahari Mai Allah, a matsayin shugaban kafintoci a sabon gari.

Shi ma jawabinsa, sabon shugaban kungiyar da aka kaddamar a wannan rana Alhaji Suleiman Yusuf, wanda aka fi kira da Na Hari Mai Akllah, ya nuna matukar jin dadinsa na yadda mambobin kungiyar suka ga dacewarsa ya zama shugaban wannan kungiya, bayan ya yi mataimakin shugaban kungiyar a shekarun baya.

Alhaji Yusuf Na Hari ya lashi takobin duk abin day a dac e kuma dokar kungiyar ta amince, domin ci gaban wannan kungiya ta kafintoci, ta yadda kuma mambobin kungiyar za su amfana da shugabancin da za a yi ma sun an da shekara hudu ma su zuwa.

Da kuma ya juya ga wadanda suka taka rawar gaban hantsi a lokacin zabubbukan da aka yi, amma ba su sami nasara ba, a nan ya sifanta su da cewar, babu abin da ke zukatansu, sai neman damar da za su hau madafun ikon da za su tallafa wa wannan kungiyar da kuma mambobin ta, ya kara da cewar, sun dab a su kai ga samun nasara ba, ya ce ya na fatan za su ba shi duk goyon baya da kuma kyawawan shawarwarin da za su tallafa wa shugabancin kungiyar da kuma mambobinta.

Sauran wadanda suka yi jawabi a wajen taron sun hada da Alhaji Abbas Tanko da Alhaji Uwaisu da kuma tsohon shugaban wannan kungiya, Alhaji Ahmed Isa Goro, inda dukkansu suka lashi takobin ci gaba da rungumar sabbin shugabannin da aka kaddamar da hannu biyu, domin su sami nasarar da ake sa wa gaba da ya shafi cigaban sana’ar kafinta da kuma mabobin kungiyar bakidaya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yobe Za Ta Gudanar Da Zaben Kananan Hukumomi Ranar 27 Ga Fabarairu

Next Post

Kananan Hukumomi: Al’ummar Tarauni Sun Yi Wa Habu P.A Ruwan Kuri’u

RelatedPosts

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

by Isa Abdullahi Gidan Bakko
7 hours ago
0

Daga Ahmed Muh'd Danasabe, Lokoja Ranar Lahadi da ta gabata...

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

by Isa Abdullahi Gidan Bakko
7 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri Biyo bayan harin da mayakan Boko...

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

by Isa Abdullahi Gidan Bakko
7 hours ago
0

Daga Musa Muhammad, Abuja An kammala dukkan shirye-shirye don fara...

Next Post
Al'ummar Tarauni

Kananan Hukumomi: Al'ummar Tarauni Sun Yi Wa Habu P.A Ruwan Kuri'u

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version