• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Mutum 15 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Filato

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
An Kashe Mutum 21 A Wani Sabon Hari A Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutane 15 ne aka tabbatar da mutuwarsu a wasu sabbin hare-hare da aka kai a kauyukan Bwai da Chisu na karamar hukumar Mangu ta jihar Filato.

LEADERSHIP ta tattaro cewa lamarin ya faru ne a daren ranar Talata lokacin da mazauna garin suka kwanta barci.

  • Aiwatar Da Alkawain Da Aka Yi Yana Da Muhimmanci
  • Gwamnan Kano Ya Mayar Da Muhyi Kan Kujerarsa

Bincike ya nuna cewa maharan sun afkawa al’ummomin biyu lokaci guda inda suka kashe mutane tare da kone gidaje.

Wani shaidan gani da ido, Bamshak Ishaya ya yi zargin cewa ‘yan bindigar Fulani ne suka kashe wasu mutane a gidan wani shugaban al’umma a kauyen Chisu a daren ranar Talata da misalin karfe 11:00 na dare.

An gano cewa an kuma kone Cocin COCIN RCC da ke Bwai da ke kan hanyar Mangu zuwa Bokkos tare da kone gidaje da motoci da babura masu kafa uku.

Labarai Masu Nasaba

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

Wakilinmu ya ruwaito cewa, al’ummar yankin sun ji karar harbe-harbe, inda suka garzaya zuwa gidan Jagoran unguwarsu, don neman mafaka.

A Bwai, baya ga Cocin, an kuma kone gidaje da ke kusa da kasuwar, sannan an kone wata mata a yankin.

A halin da ake ciki, dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Mangu ta kudu a majalisar dokokin jihar, Mista Bala Fwangje shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce, “da misalin karfe 11 na dare, mun samu waya cewa makiyaya sun shigo Chisu da Bwai, da safiyar yau ne muka ji an kashe kimanin mutane 15, an lalata gidaje, an kone dukiyoyi da dama, har yanzu ban samu cikakken bayani ba.”

Haka zalika, shugaban kwamitin riko na karamar hukumar Mangu, Mista Markus Artu, ya shaida wa manema labarai ta wayar tarho cewa lamarin ya faru amma har yanzu ba shi da cikakken bayani.

Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Filato, DSP Afred Alabo ba mu samu jin ta bakinsa ba har ya zuwa lokacin hada wannan rahoto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FilatoFulaniKisaMangu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Kano Ya Mayar Da Muhyi Kan Kujerarsa

Next Post

Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

Related

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

17 minutes ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

1 hour ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

2 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

6 hours ago
Next Post
Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.