• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rufe Babban Taron Wakilan Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Na 20

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Rufe Babban Taron Wakilan Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Na 20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Asabar aka rufe babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin(JKS) na 20 a birnin Beijing.

A yayin bikin rufe taron, wakilai 2338 mahalarta taron sun zabi kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20, da kwamitin ladabtarwa da sanya ido na kwamitin kolin.

  • Ya Kamata Amurka Ta Koyi Darasi Daga Yakin Harajin Da Bai Yi Nasara Ba Kan Sin

Kana an zartas da kuduri game da rahoton kwamitin kolin jam’iyyar JKS karo na 19, da kuduri game da rahoton ayyukan kwamitin ladabtarwa da sanya ido na kwamitin kolin karo na 19, da kuma kuduri kan gyararren kundin ka’idojin jam’iyyar.

Taron ya amince da shigar da sabbin nasarorin nazari kan tunanin shugaba Xi Jinping game da tsarin gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin a sabon zamani da ake ciki tun bayan babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 19 a cikin kundin ka’idojin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin.

Kuma bisa ga manyan ayyukan da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ta sanya gaba a babban taron wakilan JKS karo na 20, an daidaita tare da kyautata bayani kan burin da ake fatan cimmawa a kundin ka’idojin jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

An kuma tabbatar da babban burin bunkasuwar tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar Sin, wato za mu cimma nasarar zamanantar da kasar Sin mai bin tsarin gurguzu nan da shekarar 2035, da gina kasar Sin ta yadda za ta zama kasa mai karfi dake bin tsarin gurguzu na zamani nan zuwa tsakiyar wannan karni, wato yayin cika shekaru 100 da kafa jamhuriyar Jama’ar Sin.

Xi Jinping ya shugabanci bikin rufe babban taro, tare kuma da gabatar da jawabi. Inda ya jaddada cewa, jam’iyyar kwaminisanci ta kasar Sin ta shafe shekaru dari na gwagwarmaya, kuma ta bullo da wata sabuwar hanya domin daukar jarrabawar. Jam’iyyar tana da cikakken kwarin gwiwa da karfin samar da sabbin mu’ujizai da za su burge duniya a sabon zamani.

Ya kuma yi kira ga daukacin jam’iyyar da ta jagoranci al’ummomin dukkan kabilun kasar da su hada kai don gina kasa mai bin tsarin gurguzu na zamani bisa a dukkan fannoni, da kuma sa kaimi ga farfadowar al’ummar kasar Sin a dukkan fannoni. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Kasar Nan Kawanya – TY Danjuma 

Next Post

2023: APC Ba Jam’iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya – Atiku Ya Gargadi ‘Yan Nijeriya 

Related

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

2 hours ago
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

4 hours ago
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

4 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

6 hours ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

6 hours ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

8 hours ago
Next Post
2023: APC Ba Jam’iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya – Atiku Ya Gargadi ‘Yan Nijeriya 

2023: APC Ba Jam'iyyar Da Za A Goya Wa Baya Ba Ce, Sun Rusa Nijeriya - Atiku Ya Gargadi 'Yan Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.