• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

by Yusuf Shuaibu
3 hours ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu rarrabuwar kawuna a jam’iyyar ADC kan sahihancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark a yayin da wani tsagi na jam’iyyar ya nuna bai amince da shugabancin rikon kwaya ba a halin yanzu.

Wannan ya faru ne a lokacin da wani bangare na jam’iyyar da tsohon dan takarar gwamnan Jihar Gombe, Nafiu Bala yake jagoranta ya yi ikirarin cewa shugabancin rikon gwarya na Dabid Mark ba halastacce ba ne kuma ya saba wa kundin tsarin jam’iyyar.

  • Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara

A cikin wata sanarwa da mai ba da shawara na musamman ga Bala kan al’amuran jama’a, Dakta Aminu Alhassan ya Sanya wa hannu, ya ce tsagin ADC ya jaddada cewa kawai mambobi na asali wanda su ne ya kamata a bai wa jagorancn jam’iyar.

Ya ce, “Dangane da takardar murabus na Cif Ralph Nwosu, mun lura cewa wasu mutane, musamman Dabid Mark da abokansa, su ne suka yi kokarin bayyana ikirarinsu na jagorancin jam’iyyar, wanda hakan ya sab awa ka’idoji da kundin tsarin mulkin jam’iyyarmu ya shimfida.

“Da farko dai, yana da muhimmanci a fayyace cewa murabus din Ralph Nwosu ba ta haifar da yanayi mai kyau ba ga kowa da ke cikin ADC. Ma’ana, ta bude tattaunawa mai muhimmanci game da makomar jagorancinmu, tattaunawa da ya kamata a gudanar bisa tsarin da kundin tsarin mulkin jam’iyyarmu ya kafa.

Labarai Masu Nasaba

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

“Tsarin mulkin ADC ta bayyana cewa duk wanda ke neman zama shugaban jam’iyyar, dole ne ya kasance mamba nagari na jam’iyya. Wannan shi ne muhimman bukata ta asali wadda ba za a iya yin watsi da ita ko kauce mata ta kowace hanya ba.

“A cewar tsarin mulkin ADC, hanyar da ta dace don cike gurbin jagoranci bayan tafiyar Cif Nwosu ita ce, ta hanyar taron kwamitin zartarwa na kasa.”

Tsaagin jam’iyyar ta sake tabbatar da cewa Alhaji Nafiu shi ne halastaccen shugabanta na kasa tare da kira ga ‘ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali da hadin kai.

Ya kuma bayyana kwarin giwa kan ikon hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) na kiyaye ka’idojin kundin tsarin mulki da na dimokuradiyya a cikin harkokin jam’iyyar siyasa.

Ya kara da cewa, “Wannan taron zai zama dandalin tattaunawa kan hanyar ci gaba kuma za a biyo bayansa da tantancewa a matakai na gaba na taron jam’iyyar. Wannan ne inda za mu tabbatar da cewa jagorancin jam’iyyarmu an kayyade ta ne daga wadanda ke da gaske suna sha’awar ra’ayoyi da manufofin ADC.”

“Muna so mu jaddada cewa babu wani tanadi a cikin tsarin dokokin hukumar zabe da tsarin mulki ko dokokin jam’iyyar ADC da ke ba mutum damar karbar jagoranci ba tare da cika sharuddan zama mamba ba da tsarin dimokuradiyya ya tanada.

“Ayyukan da Dabid Mark da abokan huldarsa ke yi ba kawai saba wa tsarin mulkin jam’iyyarmu ba ne, yana kuma nuna rashin girmamawa ga ka’idojin dimokuradiyya da ADC ta tsayu a kai.

“Muna kira ga mambobinmu masu muhimmanci da jajircewa, ku da ku kasance cikin zaman lafiya da kuma mayar da hankali a wannan lokaci na neman samun sauye-sauye. Ci gaban da muka yi a matsayin jam’iya shaida ce ga aikin tukuru da jajircewar mambobinmu na asali.

“Dole ne mu kalubanci abubuwa marasa kyau na wadanda ke son kawo cikas ga hadin kanmu da ci gabanmu. ADC jam’iyya ce da aka gina bisa ginshikin gaskiya, hadin kai, da dabi’un dimokuradiyya, kuma dole ne mu yi aiki tare wajen kare wadannan ka’idoji.

“A daidai wannan lokaci, muna kuma son tabbatar da cewa muna da kwarin giwa kan hukumar zabe ta kasa wacce ba ta dogaro da gwamnati da shiga cikin wannan lamari. Muna yarda da sadaukarwarta wajen tabbatar da bin doka da tsari da tabbatar da cewa ana girmamawa kuma ana bin tsarin dimokuradiyya a cikin jam’iyyun siyasa. Jam’iyyar ADC ta ci gaba da jajircewa wajen yin aiki tare da INEC don inganta yanayin siyasa wanda zai kasance mai kyau tare da martaba tsarin dimokuradiyya.

“A karshe, muna goyon bayan Alhaji Nafiu a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na gaskiya. Jagorancinsa zai zama mai mutunta ka’idojin jam’iyyarmu a wannan lokaci na canji, kuma muna da tabbacin cewa zai kula da hakkin asalin mambobinmu masu daraja. Muna kira ga dukkanin ‘ya’yan jam’iyyar ADC na asali su goyi bayan Alhaji Nafiu da kuma aiki tare da shi don inganta jam’iyyarmu da al’umar da muke yi wa hidima.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Next Post

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Related

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

4 hours ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

3 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

3 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

4 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

4 weeks ago
Next Post
Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.