• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tafka Gumurzu, Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram Da Yawa, Wasu Sun Miƙa Wuya

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Tsaro
0
An Tafka Gumurzu, Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram Da Yawa, Wasu Sun Miƙa Wuya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar haɗin gwuiwa ta MNJTF ta yi nasarar kai wani sumame da ya yi sanadin miƙa wuyar ƴan ta’addar ƙungiyar IS guda uku tare da kuɓutar da mutane 34 da suka yi garkuwa da su, da suka haɗa da mata da ƙananan yara daga yankin kudancin tafkin Chadi.

Laftanar Kanal Abubakar Abdullahi, babban jami’in yaɗa labarai na rundunar soji na MNJTF, ya bayyana cewa, a ranar 15 ga watan Yuni, 2024, aikin kakkaɓe ƴan ta’addan a ƙauyukan Mazuri, Itsari, Mudu, da Maleri ya kai ga tarwatsa sansanonin ‘yan ta’adda tare da kashe wani dan tada kayar baya.

  • NDLEA Ta Cafke Mai Ciki Da Kudin Jabu Naira Miliyan 3.2
  • Yadda Ƙungiyar Matasan Arewa Kan Harkokin Tsaro Ta Shirya Tattaunawa Kan Batun ‘Yansandan Jihohi

A ranar 17 ga Yuni, 2024, mayakan ISWAP uku daga sansanin Jabilaram da ke tafkin Chadi, waɗanda aka bayyana sunayensu da Babakura Abubakar, Abacha Kyari, da Mohammad Adam, sun miƙa wuya ga dakarun sa-kai. Yanzu haka dai ana ci gaba da yi wa mayakan tambayoyi domin samun ƙarin bayanan sirri kan ayyukan ta’addanci.

Mayaƙan ISWAP da suka miƙa wuya
Wasu daga cikin waɗanda Sojoji suka ceto

Wannan ci gaban wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na raunana karfin aiki da kwarin gwiwar duk ƴan ta’adda a yankin.

A ci gaba da inganta nasarar hare-haren da aka kai a ranar 9 ga Yuni, 2024, a Kollaram, sun lalata na’urori masu fashewa da suka haɗa da ƙunar bakin wake guda uku da ke shirin kai wani gagarumin hari.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

Mayaƙan ISWAP da suka miƙa wuya
Mayaƙan ISWAP da suka miƙa wuya

Manjo Janar Ibrahim Sallau Ali, Kwamandan Rundunar MNJTF, ya yaba da bajintat sojojin tare da jaddada aniyar rundunar na kawar da ta’addanci, tabbatar da tsaron fararen hula, da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin tafkin Chadi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Alamomi 20 Na Ciwon Kansa Da Suka Kamata A Sani

Next Post

Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Afrika ta Kudu

Related

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

15 hours ago
Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
Tsaro

Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

2 weeks ago
Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
Tsaro

Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya

2 weeks ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

3 weeks ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

3 weeks ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

4 weeks ago
Next Post
Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Afrika ta Kudu

Manzon Musamman Na Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Afrika ta Kudu

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.