• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tona Asirin Ainihin Dalilin Saukar Hadimin Tinubu

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
An Tona Asirin Ainihin Dalilin Saukar Hadimin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ajuri Ngelale, mai magana da yawun Shugaba Bola Tinubu ya sanar da yin murabus daga muƙaminsa, inda ya bayyana matsalolin lafiyar iyalinsa a matsayin babban dalilin da ya sa zai ɗauki hutu na ɗan lokaci. Sai dai, wasu majiyoyi na nuna cewa akwai wani dalilin ajiye aikin nasa saɓanin yadda aka bayyana.

Rahotanni sun nuna cewa ficewar Ngelale daga fadar shugaban ƙasar ta samo asali ne daga rikice-rikicen cikin gida da rashin jituwa a tsakanin tawagar watsa labaran shugaban ƙasar.

  • Bola Tinubu Da Wasu Shugabannin Afirka Sun Iso Beijing Don Halartar Taron FOCAC
  • Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Hajiya Dada Yar’adua

Ana zargin cewa akwai matsin lamba na a sauya shi da wanda ake ganin yana da kyakkyawar alaka da manema labarai da kuma mafi dacewa da ra’ayin shugaba Tinubu.

Bugu da ƙari, yadda ya ke gudanar da ayyuka daban-daban – daga matsayinsa na mai magana da yawun shugaban ƙasa zuwa mukaman wakilin shugaban ƙasa kan sauyin yanayi da kuma shugaban kwamitin kula da aikin Project Evergreen – ya shafi aikinsa na asali a harkokin watsa labarai.

Rikicin cikin gida da sauran ma’aikatan watsa labarai, tare da yadda tasirinsa ke ƙaruwa a ɓangaren sauyin yanayi, sun ƙara janyo wannan rashin jituwa.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Lamarin ya kai ga an umarce shi ya zaɓi tsakanin ci gaba da zama mai magana da yawun shugaban ƙasa ko kuma mayar da hankali kan aikin sa na sauyin yanayi. Da ya zaɓi ci gaba da mukaminsa na mai magana da yawun shugaban ƙasa, an zargi wasu daga cikin manyan na kusa da shugaban ƙasa da yin katsalandan, wanda hakan ya janyo ajiye  dukkan mukaman nasa.

Wasu majiyoyi sun nuna cewa shugaba Tinubu na iya naɗa tsohon Shugaban Ma’aikatansa, Sunday Dare, a matsayin wanda zai maye gurbin Ngelale, duk da cewa ba a tabbatar da wannan ba.

Ngelale bai ce komai ba a fili game da wannan batu, kuma duk wani ƙoƙari na samun karin bayani daga gare shi ya ci tura kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta rawaito.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aso VillaNgelaleTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Warin Gaba  (Baginal Odor)

Next Post

Fadawa Soyayya Saboda Tausayin Budurwa Da Yadda Abin Ke Sauyawa

Related

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

2 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

4 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

6 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

19 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

23 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

1 day ago
Next Post
Fadawa Soyayya Saboda Tausayin Budurwa Da Yadda Abin Ke Sauyawa

Fadawa Soyayya Saboda Tausayin Budurwa Da Yadda Abin Ke Sauyawa

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.