ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tona Asirin Ainihin Dalilin Saukar Hadimin Tinubu

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Tinubu

Ajuri Ngelale, mai magana da yawun Shugaba Bola Tinubu ya sanar da yin murabus daga muƙaminsa, inda ya bayyana matsalolin lafiyar iyalinsa a matsayin babban dalilin da ya sa zai ɗauki hutu na ɗan lokaci. Sai dai, wasu majiyoyi na nuna cewa akwai wani dalilin ajiye aikin nasa saɓanin yadda aka bayyana.

Rahotanni sun nuna cewa ficewar Ngelale daga fadar shugaban ƙasar ta samo asali ne daga rikice-rikicen cikin gida da rashin jituwa a tsakanin tawagar watsa labaran shugaban ƙasar.

  • Bola Tinubu Da Wasu Shugabannin Afirka Sun Iso Beijing Don Halartar Taron FOCAC
  • Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Hajiya Dada Yar’adua

Ana zargin cewa akwai matsin lamba na a sauya shi da wanda ake ganin yana da kyakkyawar alaka da manema labarai da kuma mafi dacewa da ra’ayin shugaba Tinubu.

ADVERTISEMENT

Bugu da ƙari, yadda ya ke gudanar da ayyuka daban-daban – daga matsayinsa na mai magana da yawun shugaban ƙasa zuwa mukaman wakilin shugaban ƙasa kan sauyin yanayi da kuma shugaban kwamitin kula da aikin Project Evergreen – ya shafi aikinsa na asali a harkokin watsa labarai.

Rikicin cikin gida da sauran ma’aikatan watsa labarai, tare da yadda tasirinsa ke ƙaruwa a ɓangaren sauyin yanayi, sun ƙara janyo wannan rashin jituwa.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Lamarin ya kai ga an umarce shi ya zaɓi tsakanin ci gaba da zama mai magana da yawun shugaban ƙasa ko kuma mayar da hankali kan aikin sa na sauyin yanayi. Da ya zaɓi ci gaba da mukaminsa na mai magana da yawun shugaban ƙasa, an zargi wasu daga cikin manyan na kusa da shugaban ƙasa da yin katsalandan, wanda hakan ya janyo ajiye  dukkan mukaman nasa.

Wasu majiyoyi sun nuna cewa shugaba Tinubu na iya naɗa tsohon Shugaban Ma’aikatansa, Sunday Dare, a matsayin wanda zai maye gurbin Ngelale, duk da cewa ba a tabbatar da wannan ba.

Ngelale bai ce komai ba a fili game da wannan batu, kuma duk wani ƙoƙari na samun karin bayani daga gare shi ya ci tura kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta rawaito.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Fadawa Soyayya Saboda Tausayin Budurwa Da Yadda Abin Ke Sauyawa

Fadawa Soyayya Saboda Tausayin Budurwa Da Yadda Abin Ke Sauyawa

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.