ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tona Asirin Ainihin Dalilin Saukar Hadimin Tinubu

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Tinubu

Ajuri Ngelale, mai magana da yawun Shugaba Bola Tinubu ya sanar da yin murabus daga muƙaminsa, inda ya bayyana matsalolin lafiyar iyalinsa a matsayin babban dalilin da ya sa zai ɗauki hutu na ɗan lokaci. Sai dai, wasu majiyoyi na nuna cewa akwai wani dalilin ajiye aikin nasa saɓanin yadda aka bayyana.

Rahotanni sun nuna cewa ficewar Ngelale daga fadar shugaban ƙasar ta samo asali ne daga rikice-rikicen cikin gida da rashin jituwa a tsakanin tawagar watsa labaran shugaban ƙasar.

  • Bola Tinubu Da Wasu Shugabannin Afirka Sun Iso Beijing Don Halartar Taron FOCAC
  • Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Hajiya Dada Yar’adua

Ana zargin cewa akwai matsin lamba na a sauya shi da wanda ake ganin yana da kyakkyawar alaka da manema labarai da kuma mafi dacewa da ra’ayin shugaba Tinubu.

ADVERTISEMENT

Bugu da ƙari, yadda ya ke gudanar da ayyuka daban-daban – daga matsayinsa na mai magana da yawun shugaban ƙasa zuwa mukaman wakilin shugaban ƙasa kan sauyin yanayi da kuma shugaban kwamitin kula da aikin Project Evergreen – ya shafi aikinsa na asali a harkokin watsa labarai.

Rikicin cikin gida da sauran ma’aikatan watsa labarai, tare da yadda tasirinsa ke ƙaruwa a ɓangaren sauyin yanayi, sun ƙara janyo wannan rashin jituwa.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Lamarin ya kai ga an umarce shi ya zaɓi tsakanin ci gaba da zama mai magana da yawun shugaban ƙasa ko kuma mayar da hankali kan aikin sa na sauyin yanayi. Da ya zaɓi ci gaba da mukaminsa na mai magana da yawun shugaban ƙasa, an zargi wasu daga cikin manyan na kusa da shugaban ƙasa da yin katsalandan, wanda hakan ya janyo ajiye  dukkan mukaman nasa.

Wasu majiyoyi sun nuna cewa shugaba Tinubu na iya naɗa tsohon Shugaban Ma’aikatansa, Sunday Dare, a matsayin wanda zai maye gurbin Ngelale, duk da cewa ba a tabbatar da wannan ba.

Ngelale bai ce komai ba a fili game da wannan batu, kuma duk wani ƙoƙari na samun karin bayani daga gare shi ya ci tura kamar yadda jaridar Daily Nigerian ta rawaito.

Tinubu
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Fadawa Soyayya Saboda Tausayin Budurwa Da Yadda Abin Ke Sauyawa

Fadawa Soyayya Saboda Tausayin Budurwa Da Yadda Abin Ke Sauyawa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.